• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Adalci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Adalci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Litinin ne aka kaddamar da bikin makon tinkarar sauyin yanayi a nahiyar Afirka na wannan shekara ta 2022, a kasar Gabon.

Hakika batun sauyin yanayi na kara janyo hankalin jama’a, musamman ma ta yin la’akari da yadda ake samun abkuwar karin nau’o’in bala’u daga Indallahi a wurare daban daban.

  • Ya Wajaba Amurka Ta Kaucewa Sake Maimaita Irin Kuskuren Da Ta Aikata Game Da Taiwan

A shekarar da muke ciki, kasashe da dama dake nahiyar Afrika, irinsu Madagascar,da Mozambique, da Malawi, sun fuskanci radadin wani nau’i na bala’u.

Kana an gamu da matsalar ambaliyar ruwa a jihar Jigawa dake Najeriya, sai kuma jihohin Zinder, da Maradi, da Diffa a jamhuriyar Nijar.

A cewar Akinwumi Adesina, shugaban bankin raya nahiyar Afirka, matsalar sauyin yanayin duniya, ta kan haddasa asarar dalar Amurka biliyan 7 zuwa 15 a kasashen Afirka, a duk shekara.

Labarai Masu Nasaba

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Don daidaita wannan matsala, kasashen duniya sun kudiri niyyar rage fitar da iska mai dumama yanayi, tare da kulla wasu yarjeniyoyi, inda aka tanadi cewa, kasashe masu sukuni da kasashe masu tasowa, za su dauki nauyin daidaita matsalar sauyin yanayi tare, sai dai ayyukan da za su dauki nauyin gudanarwa sun sha bamban.

Wato ya kamata kasashe masu sukuni su rage fitar da iska mai dumama yanayi, da samar da kudade da fasahohi ga kasashe masu tasowa, yayin da kasashe masu tasowa ba dole ne a kayyade musu yawan iska mai dumama yanayi da za su rika fitarwa ba.

Sai dai har zuwa yanzu, ba a aiwatar da wadannan ka’idojin da kyau ba. Maimakon haka, kasar Amurka da kasashen Turai, da sauran kasashe masu sukuni, suna neman ikon jagorantar ayyukan tinkarar sauyin yanayi a duniya, don neman danka wa kasashe masu tasowa nauyi na rage fitar da iskar dake dumama yanayi. Kana sau da yawa, kasashe masu sukuni sun kasa cika alkawarin da suka yi, na samar da a kalla dala biliyan 100 ga kasashe masu tasowa a duk shekara, don tallafawa aikin tinkarar sauyin yanayi. Haka zalika, kasar Amurka ta bullo da dabaru daban daban, ciki har da na siyasa, don neman shawo kan bangaren samar da kayayyaki masu alaka da rage fitar da iska mai dumama yanayi, yayin da kasashen Turai a nasu bangare, suna fakewa da batun tinkarar sauyin yanayi, wajen daukar matakan kariyar ciniki. Dukkansu sun fi karkata ga moriyar kai fiye da moriyar bai daya ta dan Adam.

Hakika dai, babu adalci a matakan kasashen Turai da kasar Amurka. Saboda tun kafin kasashe masu tasowa su fara raya masana’antu, kasashe masu sukuni na yammacin duniya, sun kwashe kimanin shekaru 200 suna kokarin raya masana’antu tare da fitar da iska mai guba.

Kana yanzu haka kasashe masu tasowa, suna fitar da iska mai dumama yanayi ne sakamakon gudanar da masana’antu na samar da dimbin kayayyakin da kasuwannin kasashe masu sukuni ke bukata.

Ban da wannan kuma, kasashe masu tasowa, ba su da karfin daukar karin nauyin rage fitar da iska mai dumama yanayi. Haka wannan batu yake, musamman ma a kasashen Afirka.

Kamar yadda wani shahararren masani mai suna Taling Rodrigue, dan kasar Kamaru, ya fada: galibin kasashen dake nahiyar Afirka na kokarin raya kayayyakin more rayuwa, da masana’antu, inda suke tinkarar kalubaloli da yawa, musamman ma a fannonin raya tattalin arziki, da karuwar yawan al’umma. Sai dai a lokaci guda suna zama karkashin tarnakin manufofin rage fitar da iska mai dumama yanayi, wadda ta kasance iri daya da ta kasashen yamma. Wannan yanayi ya sa kasashen Afirka kasa sauke nauyin da aka dora musu na rage fitar da iskar dake dumama yanayi.

Ganin haka ya sa kasar Sin da sauran kasashe masu tasowa ke daga murya a wurare daban daban, don yin kira ga gamayyar kasa da kasa da su bullo da tsarin aiki mai adalci, don tabbatar da tushen hadin gwiwar kasashen daban daban, a fannin tinkarar matsalar sauyin yanayin duniya.

Muna jiran kasashen duniya, musamman ma kasashe masu sukuni na yammacin duniya, da su amsa wannan kira. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Lamunci Kai Hari wa Jami’anmu Ba, Gargadin Sufeton ‘Yansanda

Next Post

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Pakistan Bisa Matsanaciyar Ambaliyar Ruwa Da Ta Mamaye Wasu Sassan Kasar

Related

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

5 hours ago
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

6 hours ago
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

7 hours ago
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

9 hours ago
An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 
Daga Birnin Sin

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

10 hours ago
Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu

11 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Pakistan Bisa Matsanaciyar Ambaliyar Ruwa Da Ta Mamaye Wasu Sassan Kasar

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Pakistan Bisa Matsanaciyar Ambaliyar Ruwa Da Ta Mamaye Wasu Sassan Kasar

LABARAI MASU NASABA

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

August 14, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

August 14, 2025
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

August 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Mako Guda – DHQ

August 14, 2025
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.