• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Adalci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Adalci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Litinin ne aka kaddamar da bikin makon tinkarar sauyin yanayi a nahiyar Afirka na wannan shekara ta 2022, a kasar Gabon.

Hakika batun sauyin yanayi na kara janyo hankalin jama’a, musamman ma ta yin la’akari da yadda ake samun abkuwar karin nau’o’in bala’u daga Indallahi a wurare daban daban.

  • Ya Wajaba Amurka Ta Kaucewa Sake Maimaita Irin Kuskuren Da Ta Aikata Game Da Taiwan

A shekarar da muke ciki, kasashe da dama dake nahiyar Afrika, irinsu Madagascar,da Mozambique, da Malawi, sun fuskanci radadin wani nau’i na bala’u.

Kana an gamu da matsalar ambaliyar ruwa a jihar Jigawa dake Najeriya, sai kuma jihohin Zinder, da Maradi, da Diffa a jamhuriyar Nijar.

A cewar Akinwumi Adesina, shugaban bankin raya nahiyar Afirka, matsalar sauyin yanayin duniya, ta kan haddasa asarar dalar Amurka biliyan 7 zuwa 15 a kasashen Afirka, a duk shekara.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Don daidaita wannan matsala, kasashen duniya sun kudiri niyyar rage fitar da iska mai dumama yanayi, tare da kulla wasu yarjeniyoyi, inda aka tanadi cewa, kasashe masu sukuni da kasashe masu tasowa, za su dauki nauyin daidaita matsalar sauyin yanayi tare, sai dai ayyukan da za su dauki nauyin gudanarwa sun sha bamban.

Wato ya kamata kasashe masu sukuni su rage fitar da iska mai dumama yanayi, da samar da kudade da fasahohi ga kasashe masu tasowa, yayin da kasashe masu tasowa ba dole ne a kayyade musu yawan iska mai dumama yanayi da za su rika fitarwa ba.

Sai dai har zuwa yanzu, ba a aiwatar da wadannan ka’idojin da kyau ba. Maimakon haka, kasar Amurka da kasashen Turai, da sauran kasashe masu sukuni, suna neman ikon jagorantar ayyukan tinkarar sauyin yanayi a duniya, don neman danka wa kasashe masu tasowa nauyi na rage fitar da iskar dake dumama yanayi. Kana sau da yawa, kasashe masu sukuni sun kasa cika alkawarin da suka yi, na samar da a kalla dala biliyan 100 ga kasashe masu tasowa a duk shekara, don tallafawa aikin tinkarar sauyin yanayi. Haka zalika, kasar Amurka ta bullo da dabaru daban daban, ciki har da na siyasa, don neman shawo kan bangaren samar da kayayyaki masu alaka da rage fitar da iska mai dumama yanayi, yayin da kasashen Turai a nasu bangare, suna fakewa da batun tinkarar sauyin yanayi, wajen daukar matakan kariyar ciniki. Dukkansu sun fi karkata ga moriyar kai fiye da moriyar bai daya ta dan Adam.

Hakika dai, babu adalci a matakan kasashen Turai da kasar Amurka. Saboda tun kafin kasashe masu tasowa su fara raya masana’antu, kasashe masu sukuni na yammacin duniya, sun kwashe kimanin shekaru 200 suna kokarin raya masana’antu tare da fitar da iska mai guba.

Kana yanzu haka kasashe masu tasowa, suna fitar da iska mai dumama yanayi ne sakamakon gudanar da masana’antu na samar da dimbin kayayyakin da kasuwannin kasashe masu sukuni ke bukata.

Ban da wannan kuma, kasashe masu tasowa, ba su da karfin daukar karin nauyin rage fitar da iska mai dumama yanayi. Haka wannan batu yake, musamman ma a kasashen Afirka.

Kamar yadda wani shahararren masani mai suna Taling Rodrigue, dan kasar Kamaru, ya fada: galibin kasashen dake nahiyar Afirka na kokarin raya kayayyakin more rayuwa, da masana’antu, inda suke tinkarar kalubaloli da yawa, musamman ma a fannonin raya tattalin arziki, da karuwar yawan al’umma. Sai dai a lokaci guda suna zama karkashin tarnakin manufofin rage fitar da iska mai dumama yanayi, wadda ta kasance iri daya da ta kasashen yamma. Wannan yanayi ya sa kasashen Afirka kasa sauke nauyin da aka dora musu na rage fitar da iskar dake dumama yanayi.

Ganin haka ya sa kasar Sin da sauran kasashe masu tasowa ke daga murya a wurare daban daban, don yin kira ga gamayyar kasa da kasa da su bullo da tsarin aiki mai adalci, don tabbatar da tushen hadin gwiwar kasashen daban daban, a fannin tinkarar matsalar sauyin yanayin duniya.

Muna jiran kasashen duniya, musamman ma kasashe masu sukuni na yammacin duniya, da su amsa wannan kira. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Lamunci Kai Hari wa Jami’anmu Ba, Gargadin Sufeton ‘Yansanda

Next Post

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Pakistan Bisa Matsanaciyar Ambaliyar Ruwa Da Ta Mamaye Wasu Sassan Kasar

Related

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

14 hours ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

15 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

16 hours ago
Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya
Daga Birnin Sin

Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya

17 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

18 hours ago
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

19 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Pakistan Bisa Matsanaciyar Ambaliyar Ruwa Da Ta Mamaye Wasu Sassan Kasar

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Pakistan Bisa Matsanaciyar Ambaliyar Ruwa Da Ta Mamaye Wasu Sassan Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.