• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba Amurka Ta Kaucewa Sake Maimaita Irin Kuskuren Da Ta Aikata Game Da Taiwan

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Wajaba Amurka Ta Kaucewa Sake Maimaita Irin Kuskuren Da Ta Aikata Game Da Taiwan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duniyar yau, ba wanda ya zarce Amurka a fannin iya maida fari baki, da juyar da tunanin al’umma.

Kasa ce dake kan gaba wajen ta da husuma, da kin karbar kuskuren ta, da sauya matsaya da cin dunduniya, halayen da suka zamewa kasar dabi’a a duk lokacin da take cudanya da sassan kasa da kasa.

  • Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

To sai dai kuma, karya ba za ta tserewa gaskiya ba. Idan an kalli batun da ya shafi takaddamar zirin Taiwan, duk mai hankali zai fahimci abu ne da Amurka ta tsara domin yin tsokana.

Bisa nufinta na tabbatar da daidaito a zirin Taiwan, tun da wuri Sin ta bayyana rashin amincewa, da shirin ziyarar kakakin majalissar wakilan Amurka Nancy Pelosi, kasar Sin ta yi ta nanata mummunar illar da ziyarar ta Pelosi za ta haifar, da ma sakamakon da Amurkar za ta samu idan har Pelosi ta aiwatar da ziyarar, duk da kashedin da ya fito daga sassa daban daban.

Dokokin kasa da kasa, sun baiwa kasashe ikon mulkin kai da tsaron yankuna, kana sun haramtawa duk wata kasa tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wata. Don haka, bisa kunnen kashe da Amurka ta yi, ta aikata mummunar ta’asa, kuma Sin ba ta da zabi, illa ta mayar da martani.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Matakai daban daban da kasar Sin ta aiwatar domin mayar da martani ga waccan ziyara, na da nufin yin gargadi ne ga masu aikata ta’asa, ta yunkurin samar da ’yancin Taiwan.

Sin ta zartas da matakan kare babbar moriyarta bisa doka. Kuma matakan nata sun dace da dokokin kasa da kasa da na cikin gida.

Tun fil azal, yankin Taiwan bangare ne na kasar Sin. Kuma sakamakon tsokana daga waje, ya sa dakarun sojin kasar Sin suka gudanar da atisayen soji, da sarrafa makamai a yankunan tekun dake daura da tsibirin na Taiwan, a wani mataki na tabbatar da ikon mulkin kai, da tsaron yankunan Sin. Wannan kuma na kunshe ne cikin tanade-tanaden kundin mulkin kasar, da dokokin dake haramta yunkurin ballewa daga kasar, da ma sauran dokoki masu nasaba da hakan.

Manufar kasar Sin daya tak a duniya, muhimmiyar ka’ida ce da kasar Sin ke karewa. Don haka ya wajaba, Amurka ta koyi darasi daga matakin kuskure da Pelosi ta aikata, ta komawa hanya madaidaiciya, wadda za ta dace da manufar kasar Sin daya tak a duniya, da sanarwoyi 3 da sassan biyu suka sanyawa hannu.

Ya wajaba Amurka ta kaucewa kara yin wasu kura-kurai. Idan kuma ta ci gaba, Sin za ta maida martani yadda ya kamata. (Saminu Alhassan)

 

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Alluran Rigakafin COVID-19 Ta Haifar Da Kyakkyawan Sakamako

Next Post

Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato

Related

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

53 minutes ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

2 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

3 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

5 hours ago
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

6 hours ago
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

24 hours ago
Next Post
Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato

Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.