ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba Amurka Ta Kaucewa Sake Maimaita Irin Kuskuren Da Ta Aikata Game Da Taiwan

by CMG Hausa
4 years ago
Amurka

A duniyar yau, ba wanda ya zarce Amurka a fannin iya maida fari baki, da juyar da tunanin al’umma.

Kasa ce dake kan gaba wajen ta da husuma, da kin karbar kuskuren ta, da sauya matsaya da cin dunduniya, halayen da suka zamewa kasar dabi’a a duk lokacin da take cudanya da sassan kasa da kasa.

  • Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

To sai dai kuma, karya ba za ta tserewa gaskiya ba. Idan an kalli batun da ya shafi takaddamar zirin Taiwan, duk mai hankali zai fahimci abu ne da Amurka ta tsara domin yin tsokana.

ADVERTISEMENT

Bisa nufinta na tabbatar da daidaito a zirin Taiwan, tun da wuri Sin ta bayyana rashin amincewa, da shirin ziyarar kakakin majalissar wakilan Amurka Nancy Pelosi, kasar Sin ta yi ta nanata mummunar illar da ziyarar ta Pelosi za ta haifar, da ma sakamakon da Amurkar za ta samu idan har Pelosi ta aiwatar da ziyarar, duk da kashedin da ya fito daga sassa daban daban.

Dokokin kasa da kasa, sun baiwa kasashe ikon mulkin kai da tsaron yankuna, kana sun haramtawa duk wata kasa tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wata. Don haka, bisa kunnen kashe da Amurka ta yi, ta aikata mummunar ta’asa, kuma Sin ba ta da zabi, illa ta mayar da martani.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Matakai daban daban da kasar Sin ta aiwatar domin mayar da martani ga waccan ziyara, na da nufin yin gargadi ne ga masu aikata ta’asa, ta yunkurin samar da ’yancin Taiwan.

Sin ta zartas da matakan kare babbar moriyarta bisa doka. Kuma matakan nata sun dace da dokokin kasa da kasa da na cikin gida.

Tun fil azal, yankin Taiwan bangare ne na kasar Sin. Kuma sakamakon tsokana daga waje, ya sa dakarun sojin kasar Sin suka gudanar da atisayen soji, da sarrafa makamai a yankunan tekun dake daura da tsibirin na Taiwan, a wani mataki na tabbatar da ikon mulkin kai, da tsaron yankunan Sin. Wannan kuma na kunshe ne cikin tanade-tanaden kundin mulkin kasar, da dokokin dake haramta yunkurin ballewa daga kasar, da ma sauran dokoki masu nasaba da hakan.

Manufar kasar Sin daya tak a duniya, muhimmiyar ka’ida ce da kasar Sin ke karewa. Don haka ya wajaba, Amurka ta koyi darasi daga matakin kuskure da Pelosi ta aikata, ta komawa hanya madaidaiciya, wadda za ta dace da manufar kasar Sin daya tak a duniya, da sanarwoyi 3 da sassan biyu suka sanyawa hannu.

Ya wajaba Amurka ta kaucewa kara yin wasu kura-kurai. Idan kuma ta ci gaba, Sin za ta maida martani yadda ya kamata. (Saminu Alhassan)

 

 

 

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
Daga Birnin Sin

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Next Post
Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato

Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.