• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Abubuwan Da Suka Faru Ga Super Eagles

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
AFCON

Kawo yanzu dai an kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka da kasar Ibory Coast ta karbi bakunci kuma ta lashe gasar duk da rashin nasara da ta yi a wasanni biyu na cikin rukuni.

Abubuwa sun faru kafin da kuma bayan da tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta yi rashin nasara a wasan karshe tsakaninta da kasar Ibory Coast a yammacin ranar Lahadi, masana ke tsokaci dangane da dalilan da suka sanya Nijeriyar ta yi rashin nasara.

  • Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland
  • Gwamnonin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Tsadar Rayuwa

Mai masaukin baki kasar Ibory Coast dai ta samu nasara a kan Nijeriya ne da ci 2-1 bayan Nijeriya ta fara zura kwallo a raga a miti na 38 bayan da dan wasanta, William Troost-Ekong ya sa wa kwallon kai yayin bugun kusurwa amma bayan dan wasan Ibory Coast, Franck Kessie ya farke kwallon, sannan kuma a minti na 82 Sebastian Haller ya kara kwallo ta biyu wadda da ita ce ta bai wa Ibory Coast nasara.

Annan nasara ta kasar Ibory Coast ita ce ta katse wa Nijeriyar mafarkinta na daukar kofin gasar ta AFCON a karo na hudu, tun bayan wanda ta dauka a shekarar 2013 a Afirka ta Kudu.

Amma akwai dalilai da suka janyo wa Nijeriya wannan rashin nasara wadanda nan gaba ya zama dole a dauki mataki a kansu domin gujewa irin wannan rashin nasara a wasan karshe.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Gano lagon Nijeriya: Da farko dai Nijeriya ta doke tawagar Ibory Coast a wasansu na cikin rukuni 1- 0, inda ‘yan kasar suka yi ta nuna rashin jin dadinsu a matsayinsu na masu masaukin baki har ta kai suka yi bore ciki har da kone-kone. Hakan ya sa kungiyar ta Elephants tsayawa ta yi karatun ta-nutsu domin karantar takun wasan ‘yan Super Eagles.

Kuma wannan gano lagon Nijeriya da ita Ibory Coast ta yi tabbas ya taimaka mata wajen samun nasara kan Nijeriya

Jin tsoron wasan: Bayan cin kwallo daya tilo da ‘yan Nijeriya suka yi a minti na 38 da fara wasa sai ‘yan wasan Super Eagles suka koma suka tare a bakin raga domin tsaron gida maimakon kokarin ganin sun kara jefa kwallaye kuma wannan mataki da ‘yan wasan suka dauka ya yi wa Nijeriya illa bisa la’akari da yadda ‘yan Ibory Coast din suka yi ta kai wa Nijeriya hare-hare iri-iri su kuma Super Eagles suka koma kariya kawai.

Matsalar ‘Yan wasan tsakiya: Nijeriya ta samu matsala a jerin ‘yan wasanta na tsakiya tun ba a je ko’ina ba inda ‘yan wasan suka koma kowa yana buga abin da ya ga dama da buge-buge ba tare da basira ba.

Amma shi kansa kociyan tawagar ta Super Eagles, Jose Peseiro bai boye gaskiya ba game da wannan rashin nasarar ta kungiyar da yake jagoranta inda a hirarsa da manema labarai ya ce lallai tawagarsa tana da kyau to amma a ranar Lahadin nan Ibory Coast sun koya musu yadda ake samun nasara.

Poseiro ya kuma amince cewa ‘yan Nijeriyar ba su samu yadda suke so ba domin sun rasa kwallaye da yawa kuma bai san mene ne ya sa hakan ba, ba na tsammanin ‘yan wasansa a nutse suke a ranar.

Ya kara da cewa ‘yan wasan sun bari an keta tsaron baya, sun rasa kwallaye da yawa ta haka ne suka bar abokan hamayya suka gano lagonsu suka kuma yi ta kai musu hare-hare.

Za a iya cewa kawo yanzu dai ba a san makomar Peseiro ba bayan kammala wannan gasar ta AFCON kuma da ma dai shugaban hukumar kwallon kafa ta Nijeriya, NFF Ibrahim Musa Gusau, a kwanakin baya ya ce sai bayan kammala gasar ne za su waiwayi yarjejeniyar da suka cimma da kocin na Nijeriya dan kasar Portugal.

Wadanne Kyaututtuka Aka Lashe A Gasar?

Kofi na uku ke nan da Ibory Coast ta lashe, bayan wanda ta ci a shekarar 1992 da kuma a 2015 kuma dan wasan Ibory Coast, Simon Adingra shi ne ya lashe kyautar wanda ya fi taka rawar gani a wasan karshe a AFCON ranar Lahadi.

Kyaftin din Nijeriya, William Troost-Ekong shi ne aka bai wa kyautar fitaccen dan wasan gasar baki dayan ta bayan ya zura kwallaye hudu a gasar kuma ya buga kowanne wasa har wasan karshe.

Dan wasan tawagar Ekuatorial Guinea, Emilio Nsue Lopez shi ne ya karbi kyautar takalmin zinare a matsayin wanda ya fi cin kwallaye bayan ya zura kwallaye guda biyar a raga.

Haka kuma mai tsaron ragar Afirka ta Kudu, Ronwen Williams shi ne mai tsaron ragar da babu kamarsa a gasar kofin Afirka da aka kammala a Ibory Coast kuma ya karbi kyautar ne bayan buge fenariti hudu a wasa da Cape Berde da kuma biyu a wasa da DR Congo ta kai Afirka ta Kudu ta kare a gurbi na uku.

Bayan da Afirka ta Kudu ta yi ta uku a AFCON a bana, ita ce ta karbi kyautar wasa ba da gaba ba da ake kira Fair Play saboda a lokacin bikin da aka yi ranar Lahadi, dan kwallon Togo, Emmanuel Adebayor ne ya fito da kofin Afirka filin wasa domin bai wa Ibory Coast.

Haka kuma Shugaban Kasa, Alassane Ouattara tare da shugan CAF, Dr Patrice Motsepe da na FIFA, Gianni Infantino ne suka mika kofin ga kyaftin din Ibory Coast, Mad Gradel.

Haka kuma an yi bikin bai wa hukumar kwallon kafar Morocco tuta da cewar ita ce za ta shirya wasannin da za a yi a shekarar 2025 kuma gasa ce ta 35 a tarihin gasar ta cin kofin Afirka.

Ga jerin wadanda suka lashe kyautuka a AFCON 2023 a Ibory Coast 2023

Wadda ta lashe kofin: Cote d’Iboire. Wadda ta yi ta biyu: Nijeriya. Wadda ta kammala a mataki na uku: Afirka ta Kudu. Wadda ta yi ta hudu: Jamhuriyar Dumukradiyyar Congo

Fitatcen dan wasan gasar: William Troost-Ekong (Nijeriya). Wanda ke kan gaba a cin kwallaye: Emilio Nsue Lopez. Fitatcen mai tsaron raga: Ronwen Williams (Afirka ta Kudu) Wasa ba da gaba ba: Afirka ta Kudu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0
Wasanni

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Next Post
Liu Jianchao Ya Halarci Babban Taron Kafa Dandalin Tattaunawa Na Jam’iyyun Siyasar Kasa Da Kasa

Liu Jianchao Ya Halarci Babban Taron Kafa Dandalin Tattaunawa Na Jam’iyyun Siyasar Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
AFCON

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.