• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Abubuwan Da Suka Faru Ga Super Eagles

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
AFCON 2023: Abubuwan Da Suka Faru Ga Super Eagles
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu dai an kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka da kasar Ibory Coast ta karbi bakunci kuma ta lashe gasar duk da rashin nasara da ta yi a wasanni biyu na cikin rukuni.

Abubuwa sun faru kafin da kuma bayan da tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta yi rashin nasara a wasan karshe tsakaninta da kasar Ibory Coast a yammacin ranar Lahadi, masana ke tsokaci dangane da dalilan da suka sanya Nijeriyar ta yi rashin nasara.

  • Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland
  • Gwamnonin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Tsadar Rayuwa

Mai masaukin baki kasar Ibory Coast dai ta samu nasara a kan Nijeriya ne da ci 2-1 bayan Nijeriya ta fara zura kwallo a raga a miti na 38 bayan da dan wasanta, William Troost-Ekong ya sa wa kwallon kai yayin bugun kusurwa amma bayan dan wasan Ibory Coast, Franck Kessie ya farke kwallon, sannan kuma a minti na 82 Sebastian Haller ya kara kwallo ta biyu wadda da ita ce ta bai wa Ibory Coast nasara.

Annan nasara ta kasar Ibory Coast ita ce ta katse wa Nijeriyar mafarkinta na daukar kofin gasar ta AFCON a karo na hudu, tun bayan wanda ta dauka a shekarar 2013 a Afirka ta Kudu.

Amma akwai dalilai da suka janyo wa Nijeriya wannan rashin nasara wadanda nan gaba ya zama dole a dauki mataki a kansu domin gujewa irin wannan rashin nasara a wasan karshe.

Labarai Masu Nasaba

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Gano lagon Nijeriya: Da farko dai Nijeriya ta doke tawagar Ibory Coast a wasansu na cikin rukuni 1- 0, inda ‘yan kasar suka yi ta nuna rashin jin dadinsu a matsayinsu na masu masaukin baki har ta kai suka yi bore ciki har da kone-kone. Hakan ya sa kungiyar ta Elephants tsayawa ta yi karatun ta-nutsu domin karantar takun wasan ‘yan Super Eagles.

Kuma wannan gano lagon Nijeriya da ita Ibory Coast ta yi tabbas ya taimaka mata wajen samun nasara kan Nijeriya

Jin tsoron wasan: Bayan cin kwallo daya tilo da ‘yan Nijeriya suka yi a minti na 38 da fara wasa sai ‘yan wasan Super Eagles suka koma suka tare a bakin raga domin tsaron gida maimakon kokarin ganin sun kara jefa kwallaye kuma wannan mataki da ‘yan wasan suka dauka ya yi wa Nijeriya illa bisa la’akari da yadda ‘yan Ibory Coast din suka yi ta kai wa Nijeriya hare-hare iri-iri su kuma Super Eagles suka koma kariya kawai.

Matsalar ‘Yan wasan tsakiya: Nijeriya ta samu matsala a jerin ‘yan wasanta na tsakiya tun ba a je ko’ina ba inda ‘yan wasan suka koma kowa yana buga abin da ya ga dama da buge-buge ba tare da basira ba.

Amma shi kansa kociyan tawagar ta Super Eagles, Jose Peseiro bai boye gaskiya ba game da wannan rashin nasarar ta kungiyar da yake jagoranta inda a hirarsa da manema labarai ya ce lallai tawagarsa tana da kyau to amma a ranar Lahadin nan Ibory Coast sun koya musu yadda ake samun nasara.

Poseiro ya kuma amince cewa ‘yan Nijeriyar ba su samu yadda suke so ba domin sun rasa kwallaye da yawa kuma bai san mene ne ya sa hakan ba, ba na tsammanin ‘yan wasansa a nutse suke a ranar.

Ya kara da cewa ‘yan wasan sun bari an keta tsaron baya, sun rasa kwallaye da yawa ta haka ne suka bar abokan hamayya suka gano lagonsu suka kuma yi ta kai musu hare-hare.

Za a iya cewa kawo yanzu dai ba a san makomar Peseiro ba bayan kammala wannan gasar ta AFCON kuma da ma dai shugaban hukumar kwallon kafa ta Nijeriya, NFF Ibrahim Musa Gusau, a kwanakin baya ya ce sai bayan kammala gasar ne za su waiwayi yarjejeniyar da suka cimma da kocin na Nijeriya dan kasar Portugal.

Wadanne Kyaututtuka Aka Lashe A Gasar?

Kofi na uku ke nan da Ibory Coast ta lashe, bayan wanda ta ci a shekarar 1992 da kuma a 2015 kuma dan wasan Ibory Coast, Simon Adingra shi ne ya lashe kyautar wanda ya fi taka rawar gani a wasan karshe a AFCON ranar Lahadi.

Kyaftin din Nijeriya, William Troost-Ekong shi ne aka bai wa kyautar fitaccen dan wasan gasar baki dayan ta bayan ya zura kwallaye hudu a gasar kuma ya buga kowanne wasa har wasan karshe.

Dan wasan tawagar Ekuatorial Guinea, Emilio Nsue Lopez shi ne ya karbi kyautar takalmin zinare a matsayin wanda ya fi cin kwallaye bayan ya zura kwallaye guda biyar a raga.

Haka kuma mai tsaron ragar Afirka ta Kudu, Ronwen Williams shi ne mai tsaron ragar da babu kamarsa a gasar kofin Afirka da aka kammala a Ibory Coast kuma ya karbi kyautar ne bayan buge fenariti hudu a wasa da Cape Berde da kuma biyu a wasa da DR Congo ta kai Afirka ta Kudu ta kare a gurbi na uku.

Bayan da Afirka ta Kudu ta yi ta uku a AFCON a bana, ita ce ta karbi kyautar wasa ba da gaba ba da ake kira Fair Play saboda a lokacin bikin da aka yi ranar Lahadi, dan kwallon Togo, Emmanuel Adebayor ne ya fito da kofin Afirka filin wasa domin bai wa Ibory Coast.

Haka kuma Shugaban Kasa, Alassane Ouattara tare da shugan CAF, Dr Patrice Motsepe da na FIFA, Gianni Infantino ne suka mika kofin ga kyaftin din Ibory Coast, Mad Gradel.

Haka kuma an yi bikin bai wa hukumar kwallon kafar Morocco tuta da cewar ita ce za ta shirya wasannin da za a yi a shekarar 2025 kuma gasa ce ta 35 a tarihin gasar ta cin kofin Afirka.

Ga jerin wadanda suka lashe kyautuka a AFCON 2023 a Ibory Coast 2023

Wadda ta lashe kofin: Cote d’Iboire. Wadda ta yi ta biyu: Nijeriya. Wadda ta kammala a mataki na uku: Afirka ta Kudu. Wadda ta yi ta hudu: Jamhuriyar Dumukradiyyar Congo

Fitatcen dan wasan gasar: William Troost-Ekong (Nijeriya). Wanda ke kan gaba a cin kwallaye: Emilio Nsue Lopez. Fitatcen mai tsaron raga: Ronwen Williams (Afirka ta Kudu) Wasa ba da gaba ba: Afirka ta Kudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Kamo Hanyar Cika Burina A Harkar Fim -Zainab

Next Post

Liu Jianchao Ya Halarci Babban Taron Kafa Dandalin Tattaunawa Na Jam’iyyun Siyasar Kasa Da Kasa

Related

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa
Wasanni

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

39 minutes ago
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?
Wasanni

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

54 minutes ago
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

2 days ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

5 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

5 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

7 days ago
Next Post
Liu Jianchao Ya Halarci Babban Taron Kafa Dandalin Tattaunawa Na Jam’iyyun Siyasar Kasa Da Kasa

Liu Jianchao Ya Halarci Babban Taron Kafa Dandalin Tattaunawa Na Jam’iyyun Siyasar Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.