ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Tsadar Rayuwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP sun caccaki gwamnatin tarayya kan matsin rayuwa tare da yin kira ta kawo matakan gaggawa da za su kawar da matsalar tattalin arziki da kalubalan tsaro da ke addabar kasar nan.

Shugaban kungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed shi ya yi wannan kira lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala ganawar gwamnonin jam’iyyar adawa da ya gudana a gidan gwamnatin Jihar Oyo da ke Abuja.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

Da yake amsa tambayoyi kan tsadar rayuwa da ake ciki, gwamnan ya bayyana cewa sun goyi bayan cire tallafin man fetur da wannan gwamnati ta yi ne bisa fatan za a samu saukin rayuwa, amma lamarin ba haka yake ba.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana damuwarsa kan yadda darajar naira ke kara zubewa kasa warwar, yayin da ake ci gaba da samun tsadar rayuwa.

A cewarsa, “Lallai muna caccakan munanan manufofin gwamnatin tarayya. Amma a bangare daya kuma, mun goyi bayan wannan gwamnati na cire tallafin mai, saboda muna da tabbacin cewa hakan shi ne manufa, idan har muka hada kai, to za a samu mafita kan wannan lamari.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Amma muna ganin shi ne ya kawo faduwar daragar naira wanda ya haddasa tsadar rayuwa, inda a yanzu muke kafada da kafada da kasar Benezuela.

Saboda haka, muna hamayya da munanan manufofin gwamnatin tarayya ba tare da mun zagi kowa ba.

“Mun dauki wannan mataki ne domin ceto ‘yan Nijeriya da kuma kasar nan ta yadda za mu yi wasu abubuwa domin taimaka wa kawunanmu.”

Tun da farko, kungiyar ta jaddata manufarta na kirkiran ‘yansandar jihohi a matsayin wani taki da zai kawo karshen matsalar tsaro a Nijeriya.

“Wannan tattaunawar ta shafi sake duba yadda kasa ke ciki da kuma matsin rayuwa da ‘yan Nijeriya suka tsinci kansu a ciki sakamakon matsin tattalin arziki da kalubalan tsaro da kasar ke fuskanta. Wannan kungiyarmu tana kira ga gwamnatin tarayya ta bullo da wasu shirye-shirye da zai kunshi dukkanin gwamnatocin kasar nan domin kawo karshen lamarin.

“Gwamnonin PDP za su ci gaba da yin iya bakin kokarinsu wajen kawo karshen matsalar tsaro domin bayar da kariya ga al’ummar kasar nan. Muna jaddada aniyarmu na yin kira da a kirkiro ‘yansandar jihohi domin kaucewa duk wata hanya ta yin amfani da ofishi ba bisa ka’ida ba ga bangarorin gwamnati.

“Lallain kungiyarmu ta koka kan yadda darajar naira ya karye tare da yinkira ga hukumomin kula da kudade da su ballo da mafita,” in ji kungiyar gwamnonin PDP.

Gwamnonin PDP sun amince da kwamitin gudanarwar jam’iyyar na kasakarkashin jagorancin mukaddasin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum. Haka kuma sun bukaci kwamitin ya kira taron gaggawa na k asa ba da jimawa ba.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

Wike Zai Sake Kwace Filaye Da Dama A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.