• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
5 hours ago
3SC

Wasan da kungiyar Kano Pillars FC ta buga da Shooting Stars (3SC) ta Ibadan a gasar firimiya ta Nijeriya ya bar baya da kura bayan da 3SC ta zura kwallo a ragar Pillars a mintunan karshe na wasan, hakan ya janyo tashin hankali tsakanin magoya bayan Pillars din da yan wasan 3SC.

 

Wasan wanda aka buga ranar Lahadi 12 ga watan Oktoba, 2025, a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano, ya kare ne da ci 1-1 inda Shooting Stars ta ci kwallonta a minti na 94, hotunan bidiyo da ke yawo a yanar gizo sun nuna yadda magoya bayan kungiyar Kano Pillars suka harzuka har wasunsu na dukan yan wasan Shooting Stars da jami’an wasa a fadin filin wasan yayin da suke ta kokarin tsira da lafiyarsu.

 

Da ta ke mayar da martani kan lamarin, kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta fitar da wata sanarwa inda ta yi Allah-wadai da rashin da’a da wasu mutane suka nuna a wasan, yayinda kuma suka yabawa jami’an tsaro da suka yi gaggawar shiga tsakani, a cewar sanarwar mai dauke da sa hannun jami’in yada labarai na kungiyar, Abubakar Isa Dandago, wasu bata-gari ne suka haddasa matsalar bayan kammala wasan, amma jami’an tsaro da masu kula da filin wasan suka shiga tsakani da wuri.

LABARAI MASU NASABA

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka

 

Sanarwar ta kara da cewa, “mun yi farin cikin ganin cewar yan wasan kungiyoyin biyu da jami’an wasan duk sun bar filin wasan ba tare da samun wani rauni ba kuma jami’an tsaro suka yi musu rakiya, kungiyar ta kara da cewa an kama wasu da dama da ake zargi da hannu a rikicin tare da mika su ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

 

Kungiyar ta jaddada kudirinta na tabbatar da zaman lafiya da da’a, kungiyar ta jaddada cewa za ta ci gaba da tabbatar da ingancin wasan kamar yadda hukumar NPFL da hukumar kwallon kafar Najeriya NFF ta tanada, Pillars ta kuma yi kira ga magoya bayanta da su gudanar da ayyukansu cikin lumana tare da ci gaba da ba kungiyar goyon baya, amma kuma wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yan wasan 3SC da aka jikkata tareda raunuka a jikinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Wasanni

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

October 12, 2025
Kofin Duniya
Wasanni

Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka

October 12, 2025
Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola
Wasanni

Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola

October 12, 2025
Next Post
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma'adanai - Minista

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.