• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

by Abubakar Abba
6 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani sabon rahoto da Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar, ya nuna cewa; fannin aikin noma a zango na hudu a 2024, ya sauka; musamman idan aka kwatanta da wanda aka samu a 2023.

Sai dai, a cewar wata kididdiga kan tattalin arzikin kasa da aka fitar a ranar Talata ta nun cewa; fannin aikin noma na kasar, ya samu karin kimanin kashi 1.17 a zango na hudu.

  • Matsalar Wuta Ta Jefa Wasu Sassan Nijeriya Cikin Duhu
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kammala Tsare-Tsaren Bunkasa Rundunar Sojin Kasar Sin Na Shekaru 5 Cikin Nasara

Wannan sabon rahoto da Hukumar ta fitar, ya nuna cewa; fannin aikin noman, ya karu da kashi 1.17, inda wannan karuwar ta nuna cewa, ta dara da kashi 1.14 da aka samu a zango na uku na shekarar 2024.

Kazalika, wannan karuwa da aka samu a zangon na hudun, ta dara wadda aka samu a zango na hudun shekarar 2023, inda aka samu kashi 2.10.

Bugu da kari, rahoton ya nuna cewa; an samu karin da ya kai kashi 1.19 a zango na hudu na 2024, idan aka kwatanta da kashi 1.13 da aka samu a 2023.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Wasu kwararru a fannin na aikin noman, sun alakanta samun wannan karuwar, saboda dauki daban-daban da gwamnatin tarayya ta samar ga fannin, musamman wajen kokarinta na rage kalubalen rashin tsaro.

Daga cikin wannan daukin na gwamnati, sun hada da kirkiro da shirin jami’an tsaro na sintiri sama da 1,000 da aka tura zuwa kanannan hukumomi 19 a 2024, don bai wa manoma da amfanin noma da aka shuka kariya, inda shirin ya taimaka wajen kara bunkasa aikin noma.

A cewar Hukumar ta ‘NBS’, fannin aikin noma ya samar da kashi 25.59 wajen habaka fannin tattalin arzikin kasar, wato ma’ana, a zango na uku na 2023, gudunmawar da fannin ya samar ga tattalin arzikin kasar, ya tsaya ne a kashi 26.11, idan aka kwatanta da gudunmawar da fannin ya samar ga tattalin arzikin kasar a 2024, wacce ta kai kashi 26.11.

Fannin aikin noman kasar, ya ci gaba da kasancewa kan gaba, musamman a bangaren day a shafi tattalin arzikin Nijeriya, duba da yadda daukacin fannin ya samar karuwar da ta kai kashi 90.70 cikin 100.

Haka zalika, a 2023, an samu raguwa da kshi biyu tare kuma da samun wata raguwar da ta kai kashi 3.86 a zango na hudu na 2023.

Daga shekara zuwa shekara, tattalin arzikin Nijeriya ya karu da kashi 3.84, wato a zango na hudu na 2024, wanda ya dara da kasshi 3.46 da aka samu a 2023.

“Kokarin da aka samu a fannin habaka tattalin arzikin kasar a zango na hudu na 2024, ya samu ne saboda garanbawul da aka yi wa fannin, inda aka samu karuwar da ta kai kashi 5.37, wanda hakan ya kara tallafawa fannin bunkasa tattalin arzikin kasar”, in ji rahoton.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwararru Sun Nuna Fargaba Kan Yadda Wasu Makiyaya Ke Bai Wa Dabbobinsu Magunguna Barkatai

Next Post

BUK Ta Kori Ɗalibai 62, Ta Dakatar da 17 Saboda Satar Jarrabawa

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

1 week ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

1 week ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

3 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

3 weeks ago
Next Post
BUK Ta Kori Ɗalibai 62, Ta Dakatar da 17 Saboda Satar Jarrabawa

BUK Ta Kori Ɗalibai 62, Ta Dakatar da 17 Saboda Satar Jarrabawa

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

September 2, 2025
Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

September 2, 2025
Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

September 2, 2025
Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

September 2, 2025
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

September 2, 2025
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

September 2, 2025
NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.