ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

by Sulaiman and Abubakar Abba
4 weeks ago
Dabbobi

Gwamnatin Jihar Taraba, ta bayyana kudurinta na yi wa kasuwannin sayar da dabbobi guda tara na jihar garanbawul tare da kuma gyara mayankar dabbobi biyar da ke jihar.

 

Hakan na daga cikin kokarin da gwamnatin ke yi na samar da dabaru, domin cin gajiyar da ke fannin.

ADVERTISEMENT
  • An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba
  • Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Kwamishinan Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci na jihar, Farfesa Nicholas Oliber Namessan, ya sanar da hakan ne inda ya ce; aikin zai taimaka wajen inganta tsafta da kuma kula da lafiyar dabbobin.

 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

Ya kara da cewa, Allah ya albarkaci Jihar Taraba da dimbin dabbobi, wanda kuma gwamnatin jihar za ta yi dukkan mai yiwuwa, wajen samar da kayan aiki tare da kara bunkasa fannin kiwo na jihar.

 

Kazalika, ya sanar da cewa; gwamnatin za kuma ta tabbatar da ta kara bunkasa kasuwancin fannin, musamman domin wadanda suke a fannin su kara samun kudaden shiga tare da kuma kara samar wa da gwamnatin kudaden shiga.

 

Nicholas, ya sanar da hakan ne, ta bakin wakilinsa Daraktan Kula da Harkokin Dabbobi da ke Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci na jihar, Daudu A. Mbaamo

 

Kwamishinan ya ci gaba da cewa, har yanzu fannin aikin noma, da shi jihar ta dogara a kai, musamman duba da cewa; fannin na bayar da gudumawa wajen kara samar da wadataccen abinci a jihar da kuma kara samar da ayyukan yi.

 

Haka zalika, ya koka da cewa; duk a irin wadannan dimbin albarkatun noma da kuma yawan dabbobin da Allah ya wadaci jihar da su, amma har yanzu jihar na ci gaba da fuskantar kalubalen karancin kasuwannin sayar da dabbobin.

 

Kwamishinan ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta himmatu, wajen kara habaka fannin kiwon jihar, wanda tuni ta tuntubi ‘yan kwangilar da za su yi aikin gyaran mayankar tare kuma da samar da kayan aiki na bunkasa kiwon dabbobi a jihar.

 

“Fannin kiwon dabbobi, na daya daga cikin fannonin da ke habaka tattalin arzikin Jihar Taraba da samar da wadataccen abinci da samar da ayyukan yi da kuma kara samar da kudaden shiga, “ a cewar Kwamishinan.

 

“Hakan ne ya sanya gwamnatin jihar, za ta samar da kayan aiki a fannin kiwon jihar, musamman domin cin gajiyar da ake da ita, daga fannin wanda kuma hakan zai amfanar da al’ummar jihar, in ji Nicholas.

 

A jawabinsa tun da farko, jami’in aikin tallafa wa kiwon dabbobi na L-PRES Hananiah Albert, ya jaddda kudurin aikin wajen ganin an cimma burin da aka sanya a gaba.

 

“Za mu tabbatar da mun bi dukkannin ka’idojin da suka dace, wajen wanzar da wannan aiki, domin cimma nasarar da aka sanya a gaba, “in ji Albert.

 

Ya kara da cewa, manufar aikin ita ce; domin mayar da hankali wajen habaka fannin hada-hadar kasuwancin kiwon na dabbobi da kuma kara bunkasa tattalin arzikin fannin tare da tabbatar da kula da lafiyar dabbobi a fadin jihar.

 

A cewarsa, a yanzu haka; akwai sama da kasuwannin sayar da dabbobi goma da ake gudanar da hada-hadar a kowane mako, wanda kuma suke da bukatar a yi musu garanbawu domin samar da saukin gudanar da yin hada-hada a cikinsu tare da kuma samar da tsaro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.