• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Alamar Tambaya A Sake Lalacewar Matatar Mai Ta Fatakwal A Karo Na 2, Bayan Kashe Dala Biliyan 1.5

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Akwai Alamar Tambaya A Sake Lalacewar Matatar Mai Ta Fatakwal A Karo Na 2, Bayan Kashe Dala Biliyan 1.5
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan an sake rufe matatar man fetur ta Fatakwal a cikin watanni biyar, mutane da dama a Nijeriya, ciki har da Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC), Ƙungiyoyin farar hula (CSOs), da kuma masana a fannin mai, sun yi kira ga waɗanda ke kula da wannan kamfani na gwamnati su yi bayani.

A watan Disamba na shekarar 2024, wata jarida ta ruwaito cewa masana’antar ta daina aiki bayan ba a daɗe da ta fara samar da kayayyaki ba. Rahoton ya nuna cewa an daina fitar da man fetur a ranar Juma’a, 13 ga Disamba, inda duk wuraren shigar da man fetur a sabuwar masana’antar suka kasance babu kowa.

LEADERSHIP ta na sane cewa kusan wata guda kafin haka, a ranar Talata, 26 ga Nuwamba, 2024, tsohon shugaban kamfanin Mai na Nijeriya (NNPCL), Mele Kyari, ya ƙaddamar da wannan masana’antar mai samar da ganga 60,000 a kowace rana, inda mutane suka yi farin ciki da hakan. Amma yanzu, sake rufe masana’antar don gyare-gyare ya haifar da tambayoyi game da yadda gwamnati ke sarrafa matatun man fetur na ƙasar.

Masana da masu sharhi a fannin shari’a sun nuna rashin gamsuwa a cikin gudanar da ayyukan masana’antun. Kamar yadda LEADERSHIP ta fahimta, akwai babban giɓi a aikin sa ido da ya kamata hukumar kula da masana’antar ta yi. Taiwo Ogunloye, wani masani a fannin makamashi kuma lauya mai ilimin fasaha, ya shaida wa wakilinmu cewa rashin bayar da rahoton bincike game da masana’antun daga hukumar kula da harkokin Mai ta Nijeriya (NMDPRA) ya haifar da shakku game da gudanar da su.

Ogunloye ya ce, sashi na 32 na Dokar Masana’antar Mai (PIA) ya bai wa hukumar ikon yin bincike kan matatun da kuma bayar da ƙa’idojin aiki. Ya ƙara da cewa rashin sa hannun hukumar ya ɗora nauyi kan NNPCL, saboda jama’a ba su san halin da matatun ke ciki ba. Ya kuma nuna damuwarsa game da rashin bayyana ainihin dalilin rufewar waɗannan matatun mai da gwamnati ta kashe kuɗaɗe masu yawa wajen gyarawa.

Labarai Masu Nasaba

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

“Ina ganin ya kamata NNPCL ta bayyana matsalolin da ke tattare da masana’antun, ta kuma nuna musamman waɗanne sassa suka shafa, domin mutane su iya tantance ingancin gudanar da su,” in ji shi. Eche Idoko, kakakin Kungiyar masu tace man Fetur ta Nijeriya (CORAN), shi ma ya kuka game da zargin rashin gaskiya, yana mai cewa jama’a ba su da masaniya game da yanayin da masana’antar take ciki.

Idoko ya yi kira da a sake bincikar kuɗaɗen da gwamnati ta kashe wajen gyara masana’antar NNPCL. A cewarsa, duk da tallafin gwamnati, farashin kayayyakin da masana’antar ta NNPCL ke fitarwa ya fi na masana’antar Dangote tsada. Ya ce CORAN ta kasance tana neman a ba da dama ɗaya ga duk masu haƙo man fetur, kuma ya yi kira da gwamnati ta ba da tallafi ga sauran masu tace man fetur masu zaman kansu.

A wani ɓangaren, Henry Adigun, mai sharhi kan harkokin yau da kullum kuma masani a fannin makamashi, ya ce bai kamata a ɗauki gyaran da NNPCL ta yi na yau da kullum ba a matsayin abin mamaki. Ya bayyana cewa, tun da matatar ta daɗe tana hutun aiki, to ana sa ran za a gano matsaloli bayan gyara, kuma za a gyara su yayin da suke tasowa. “Ya kamata mu fahimci cewa tsohuwar masana’anta ce, ba sabuwa ba, don haka ya kamata a yi gyare-gyaren da suka dace,” in ji shi.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa NNPCL ta sanar da rufewa masana’antar Fatakwal don gyara tun daga ranar 24 ga Mayu. A cewar Femi Shoneye, Babban Jami’in Sadarwa na kamfanin, za a yi wannan gyaran na tsawon wata guda, kuma kamfanin yana aiki tare da masu ruwa da tsaki don tabbatar da inganci da gaskiya. “Muna aiki tare da duk masu ruwa da tsaki, ciki har da hukumar kula da harkokin Mai ta Nijeriya, don tabbatar da cewa an yi gyaran da ya dace,” in ji shi.

Jama’a sun yi mamakin sanarwar farfaɗo da masana’antar a ƙarshen shekarar da ta gabata. Masana’antar, mai samar da ganga 60,000 a rana, tana aiki da kashi 70 cikin 100 na ƙarfinta. Farfadowarta ta kasance wani muhimmin mataki na rage dogaro da Nijeriya ke yi kan shigo da man fetur. Gwamnatin Nijeriya ta amince da gyaran masana’antar kan kuɗi dalar biliyan 1.5 a shekarar 2021.

Masana’antar tana samar da lita miliyan 1.4 na man fetur, lita miliyan 1.5 na dizal, lita miliyan 2.1 na mai mai nauyi, lita 900,000 na Kananzir, da kuma iskar gas (LPG). Farfadowarta ta kasance muhimmin mataki na samun ‘yancin cin gashin kanta a fannin makamashi da kuma ci gaban tattalin arziƙi.

NLC: “Masana’antar Ba ta Aiki”

Chris Onyeka, mataimakin sakataren NLC, ya ce dama cab NNPCL ba ta aiki don haka ba zai yiwu a ce an rufe abin da baya aiki ba. Ya ce, “Gwamnati tana ɗaukar jama’ar Nijeriya a matsayin basu san me suke ba; ba su da gaskiya, kuma muna ganin suna ɓatawa kansu suna ne da gangan. Ta yaya za su ce masana’antar Fatakwal tana aiki, tare da ta Dangote, amma har yanzu muna shigo da man fetur?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FatakwalOilPort Harcourt
ShareTweetSendShare
Previous Post

Amarya Ta Kashe Uwargida Bayan Ta Daɓa Mata Wuƙa A Katsina

Next Post

Rikici Ya Ɓarke Tsakanin ‘Yansanda Da Matasa A Rano, Mutum 1 Ya Mutu, An Harbi Wasu

Related

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

4 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

1 day ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

1 day ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

1 day ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

1 day ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

2 days ago
Next Post
Rikici Ya Ɓarke Tsakanin ‘Yansanda Da Matasa A Rano, Mutum 1 Ya Mutu, An Harbi Wasu

Rikici Ya Ɓarke Tsakanin 'Yansanda Da Matasa A Rano, Mutum 1 Ya Mutu, An Harbi Wasu

LABARAI MASU NASABA

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.