• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai ‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 13 Da Ke Da Asusun Banki Ba Su Da BVN, In Ji CBN

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A Nijeriya an yi hasashen cewa akwai kimanin mutum miliyan 200 na yawan ‘yan kasar, an bayyana cewa a cikin wadannan adadi akwai sama da mutum miliyan 70 da ke da asusun banki a bankunan kasuwancin Nijeriya.

Cikin wadannan suke da asusun bankin, akwai ‘yan Nijeriya sama da miliyan 57 da ke da asusun banki kuma suna da lambar BVN, sai dai akwai sama da ‘yan Nijeriya 13 da suna amfani da asusun banki amma ba su da BVN.

  • Kwastam Ta Kama Kayan Miliyan 55 A Adamawa

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi hadin gwiwa da hukumar daidaita alaka a tsakanin bankunan Nijeriya (NIBSS) da kwamitin masu bankuna da kuma masu ajiya a bankuna domin kaddamar da aikin samar da lambar BVN a watan Fabrairun 2014.

An kirkiro lambar BVN ne ga masu mu’amula da bankunan Nijeriya domin tantance su wajen rage damfarar kudade da inganta gudanar da ayyukan bankuna a kasar.

Tun bayan bullo da lamarin, BVN ya kasance yana da matukar muhimmin wajen abubuwan da ake bukata don budewa da kuma kula da asusun banki a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ne ya bayyana haka a birnin Kalaba wajen taron kara wa juna sani karo na 34 na masu aiko da rahotannin kudade da kuma editocin harkokin kasuwanci.

Emefiele wanda ya samu wakilcin Daraktan Sashen Kayyade Kudade na CBN, Dakta Hassan Mahmoud ya ce, “Har a zuwa ranar 31 ga Maris ta 2023, jimillar wadanda suke da BVN a Nijeriya guda 57,431,355, kuma BVN yana taimakawa wajen bunkasa harkokin ijiya a bankuna, wanda hakan zai taimaka don inganta damar samun rance ga masu karbar bashin bankuna.”

Gwamnan CBN ya kara da cewa BVN zai ci ci gaba da zama lambar tantance asusun banki da ke bukatar a matsayin wani bangare na shirye-shiryen saukaka wahalhalun da ke tattare da rashin tantance kwastomomin bankuna.

Ya ce CBN zai ci gaba da tallafa wa kwastomomin banki da ba su BVN domin su mallaki lambar ta saukakkiyar hanya.
Emefiele ya kara da cewa an gabatar da tsarin biyan kudi na PSB 2025 domin fadada hanyoyin biyan kudade ga abokan ciniki da kuma karfafa kula da tsarin biyan kudi.

Da yake karin haske game da tsarin biyan kudin, gwamnan CBN ya bayyana cewa babban bankin yana amfani da tsarin biyan kudi a matsayin wata hanyar samun nasara a harkokin kudade da kasar nan ta saka a gaba.

Bincike ya nuna cewa kashi 34 ne na ‘yan Nijeriya ke da asusun banki, kuma kashi 9 ne kacal ke iya gudanar da hada-hadar kudade ta hanyar fasahar zamani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tataburzar Hana Shigo Da Taliyar ‘Yan Yara Daga Waje Za Ta Zama Alheri Ga Nijeriya

Next Post

Tinubu Zai Fuskanci Bore Kan Tsayar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisa Da Tajudden A Matsayin Kakaki

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

9 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

11 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

12 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

12 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

16 hours ago
Next Post
Tinubu Zai Fuskanci Bore Kan Tsayar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisa Da Tajudden A Matsayin Kakaki

Tinubu Zai Fuskanci Bore Kan Tsayar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisa Da Tajudden A Matsayin Kakaki

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.