• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Yiwuwar Majalisa Ta Gyara Tsarin Mulki Don Bai Wa INEC Damar Zaben Kananan Hukumomi

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Siyasa
0
Akwai Yiwuwar Majalisa Ta Gyara Tsarin Mulki Don Bai Wa INEC Damar Zaben Kananan Hukumomi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai yiwuwar majalisar kasa ta yi wa kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 kwaskwarima domin samar da kofar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) za ta iya gudar da zaben kananan hukumomi kai tsaye, ba hukumar zabe na jihohi ba.

Wannan na zuwa ne bayan hukuncin kotun koli wacce ta bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kansu, sakamakon karar da gwamnatin tarayya ta shigar a gabanta.

Da yake mayar da martini kan lamarin lokacin taron ‘yan jarida a Abuja, dan majalisan dattawa mai makiltar Kogi ta yamma, Sunday Karimi ya bayyana cewa majalisa za ta tabbatar da cewa gwamnonin jihohi sun yi bara’a ga hukuncin kotun koli tare da gyara kundin tsarin mulki domin shigar da sabbin batutuwa.

  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Digirin Bogi A Nijeriya – Minista
  • Tsadar Rayuwa: ‘Yan Majalisa Sun Rage Albashinsu Da Kashi 50 Cikin 100

Dan jamalisar ya ce, “Cikin abubuwan da za a gyara akwai mayar da gudanar da zabe karkashin hukumar zabe ta kasa daga wurin hukumomin zabe na jihohi.”

Sanatan ya kara da cewa har yanzu tsugue ba ta kare ba, domin wasu gwamnonin za su kalubalanci lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

“Shugaban kasa Bola Tinubu ya sakar wa bangaren shari’a mara wajen gudanar da wannan shari’a ba tare da la’akari da cewa yana zangon farko ne na shugabancin kasa wanda zai so ya kara yin zago na biyu a 2027,” in ji Karimi.

Kazalika, dan majalisan dattawa mai wakiltar Delta ta tsakiya, Okakuro Ede Dafinone ya ce bisa samun wannan ci gaban, za a yi wa kundin tsarin mulkin Nijeriya kwaskwarima, domin bai wa INEC daman gudanar da zaben kananan hukumomi kai tsaye a hukumance.

Ya ce “Abun takaici ne a ce mutane ba sa amfana da tsarin dimokuradiyyarmu sakamakon yadda gwamnoni suka ki sakar wa kananan hukumomi mara wajen bari a zabi kansiloli da shugaban kananan hukumomi.

“Gwamnoninmu ne suke zaben shugabannin kananan hukumomi da kansu a jihohinsu. Idan a ce INEC za ta gudanar da zabe kamar yadda gwamnoni suke zaben kananan hukumomin, da yawa daga cikinsu ba za su zama gwamnoni ba a yau.

“Ina tunanin wanna shi ne karo na farko a tarihin kasar nan da kuma dimokuradiyyarmu, za mu yi watsi da bambancin siyasa wajen hada kai mu yi aiki tare domin gyara wani bangare na tsarin mulkinmu wajen ceto kananan hukumomi daga hannun gwamnoninmu.

“Ina yaba wa kokarin Shugaban kasa Bola Tinubu bisa wannan tunani na tabbatar da ‘yancin kananan hukumomin kasar nan.

“Za mu yi aiki da tsarin dimokuradiyya a matakin kananan hukumomi wajen tabbatar da INEC ta gudanar da zaben kananan hukumomi a fadin kasar nan, domin bai wa mutanenmu damar shiga harkokin gwamnatin dimokuradiyya.”

Sanata Dafinone siffanta zaben kananan hukumomin da ya gudana a Jihar Delta a matsayin abun kunya ga tsarin dimokuradiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: dokokinGodswill Akpabiomajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Raguwar Rikicin Manoma Da Makiyaya A Jihar Gombe

Next Post

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

Related

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
Labarai

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

12 hours ago
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC
Siyasa

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

16 hours ago
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12
Siyasa

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

1 day ago
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
Siyasa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

2 days ago
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
Siyasa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

3 days ago
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
Siyasa

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

3 days ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.