• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Yiwuwar Majalisa Ta Gyara Tsarin Mulki Don Bai Wa INEC Damar Zaben Kananan Hukumomi

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Siyasa
0
Akwai Yiwuwar Majalisa Ta Gyara Tsarin Mulki Don Bai Wa INEC Damar Zaben Kananan Hukumomi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai yiwuwar majalisar kasa ta yi wa kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 kwaskwarima domin samar da kofar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) za ta iya gudar da zaben kananan hukumomi kai tsaye, ba hukumar zabe na jihohi ba.

Wannan na zuwa ne bayan hukuncin kotun koli wacce ta bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kansu, sakamakon karar da gwamnatin tarayya ta shigar a gabanta.

Da yake mayar da martini kan lamarin lokacin taron ‘yan jarida a Abuja, dan majalisan dattawa mai makiltar Kogi ta yamma, Sunday Karimi ya bayyana cewa majalisa za ta tabbatar da cewa gwamnonin jihohi sun yi bara’a ga hukuncin kotun koli tare da gyara kundin tsarin mulki domin shigar da sabbin batutuwa.

  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Digirin Bogi A Nijeriya – Minista
  • Tsadar Rayuwa: ‘Yan Majalisa Sun Rage Albashinsu Da Kashi 50 Cikin 100

Dan jamalisar ya ce, “Cikin abubuwan da za a gyara akwai mayar da gudanar da zabe karkashin hukumar zabe ta kasa daga wurin hukumomin zabe na jihohi.”

Sanatan ya kara da cewa har yanzu tsugue ba ta kare ba, domin wasu gwamnonin za su kalubalanci lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

“Shugaban kasa Bola Tinubu ya sakar wa bangaren shari’a mara wajen gudanar da wannan shari’a ba tare da la’akari da cewa yana zangon farko ne na shugabancin kasa wanda zai so ya kara yin zago na biyu a 2027,” in ji Karimi.

Kazalika, dan majalisan dattawa mai wakiltar Delta ta tsakiya, Okakuro Ede Dafinone ya ce bisa samun wannan ci gaban, za a yi wa kundin tsarin mulkin Nijeriya kwaskwarima, domin bai wa INEC daman gudanar da zaben kananan hukumomi kai tsaye a hukumance.

Ya ce “Abun takaici ne a ce mutane ba sa amfana da tsarin dimokuradiyyarmu sakamakon yadda gwamnoni suka ki sakar wa kananan hukumomi mara wajen bari a zabi kansiloli da shugaban kananan hukumomi.

“Gwamnoninmu ne suke zaben shugabannin kananan hukumomi da kansu a jihohinsu. Idan a ce INEC za ta gudanar da zabe kamar yadda gwamnoni suke zaben kananan hukumomin, da yawa daga cikinsu ba za su zama gwamnoni ba a yau.

“Ina tunanin wanna shi ne karo na farko a tarihin kasar nan da kuma dimokuradiyyarmu, za mu yi watsi da bambancin siyasa wajen hada kai mu yi aiki tare domin gyara wani bangare na tsarin mulkinmu wajen ceto kananan hukumomi daga hannun gwamnoninmu.

“Ina yaba wa kokarin Shugaban kasa Bola Tinubu bisa wannan tunani na tabbatar da ‘yancin kananan hukumomin kasar nan.

“Za mu yi aiki da tsarin dimokuradiyya a matakin kananan hukumomi wajen tabbatar da INEC ta gudanar da zaben kananan hukumomi a fadin kasar nan, domin bai wa mutanenmu damar shiga harkokin gwamnatin dimokuradiyya.”

Sanata Dafinone siffanta zaben kananan hukumomin da ya gudana a Jihar Delta a matsayin abun kunya ga tsarin dimokuradiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: dokokinGodswill Akpabiomajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Raguwar Rikicin Manoma Da Makiyaya A Jihar Gombe

Next Post

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

7 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

11 hours ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

3 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

3 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

5 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

6 days ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.