• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Yiwuwar Majalisa Ta Gyara Tsarin Mulki Don Bai Wa INEC Damar Zaben Kananan Hukumomi

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Siyasa
0
Akwai Yiwuwar Majalisa Ta Gyara Tsarin Mulki Don Bai Wa INEC Damar Zaben Kananan Hukumomi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai yiwuwar majalisar kasa ta yi wa kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 kwaskwarima domin samar da kofar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) za ta iya gudar da zaben kananan hukumomi kai tsaye, ba hukumar zabe na jihohi ba.

Wannan na zuwa ne bayan hukuncin kotun koli wacce ta bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kansu, sakamakon karar da gwamnatin tarayya ta shigar a gabanta.

Da yake mayar da martini kan lamarin lokacin taron ‘yan jarida a Abuja, dan majalisan dattawa mai makiltar Kogi ta yamma, Sunday Karimi ya bayyana cewa majalisa za ta tabbatar da cewa gwamnonin jihohi sun yi bara’a ga hukuncin kotun koli tare da gyara kundin tsarin mulki domin shigar da sabbin batutuwa.

  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Digirin Bogi A Nijeriya – Minista
  • Tsadar Rayuwa: ‘Yan Majalisa Sun Rage Albashinsu Da Kashi 50 Cikin 100

Dan jamalisar ya ce, “Cikin abubuwan da za a gyara akwai mayar da gudanar da zabe karkashin hukumar zabe ta kasa daga wurin hukumomin zabe na jihohi.”

Sanatan ya kara da cewa har yanzu tsugue ba ta kare ba, domin wasu gwamnonin za su kalubalanci lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

“Shugaban kasa Bola Tinubu ya sakar wa bangaren shari’a mara wajen gudanar da wannan shari’a ba tare da la’akari da cewa yana zangon farko ne na shugabancin kasa wanda zai so ya kara yin zago na biyu a 2027,” in ji Karimi.

Kazalika, dan majalisan dattawa mai wakiltar Delta ta tsakiya, Okakuro Ede Dafinone ya ce bisa samun wannan ci gaban, za a yi wa kundin tsarin mulkin Nijeriya kwaskwarima, domin bai wa INEC daman gudanar da zaben kananan hukumomi kai tsaye a hukumance.

Ya ce “Abun takaici ne a ce mutane ba sa amfana da tsarin dimokuradiyyarmu sakamakon yadda gwamnoni suka ki sakar wa kananan hukumomi mara wajen bari a zabi kansiloli da shugaban kananan hukumomi.

“Gwamnoninmu ne suke zaben shugabannin kananan hukumomi da kansu a jihohinsu. Idan a ce INEC za ta gudanar da zabe kamar yadda gwamnoni suke zaben kananan hukumomin, da yawa daga cikinsu ba za su zama gwamnoni ba a yau.

“Ina tunanin wanna shi ne karo na farko a tarihin kasar nan da kuma dimokuradiyyarmu, za mu yi watsi da bambancin siyasa wajen hada kai mu yi aiki tare domin gyara wani bangare na tsarin mulkinmu wajen ceto kananan hukumomi daga hannun gwamnoninmu.

“Ina yaba wa kokarin Shugaban kasa Bola Tinubu bisa wannan tunani na tabbatar da ‘yancin kananan hukumomin kasar nan.

“Za mu yi aiki da tsarin dimokuradiyya a matakin kananan hukumomi wajen tabbatar da INEC ta gudanar da zaben kananan hukumomi a fadin kasar nan, domin bai wa mutanenmu damar shiga harkokin gwamnatin dimokuradiyya.”

Sanata Dafinone siffanta zaben kananan hukumomin da ya gudana a Jihar Delta a matsayin abun kunya ga tsarin dimokuradiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: dokokinGodswill Akpabiomajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Raguwar Rikicin Manoma Da Makiyaya A Jihar Gombe

Next Post

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

Related

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

2 hours ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

2 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

3 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

4 days ago
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan
Tattaunawa

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

4 days ago
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
Siyasa

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

5 days ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

LABARAI MASU NASABA

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.