ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Yiwuwar Majalisa Ta Gyara Tsarin Mulki Don Bai Wa INEC Damar Zaben Kananan Hukumomi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majalisa

Akwai yiwuwar majalisar kasa ta yi wa kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 kwaskwarima domin samar da kofar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) za ta iya gudar da zaben kananan hukumomi kai tsaye, ba hukumar zabe na jihohi ba.

Wannan na zuwa ne bayan hukuncin kotun koli wacce ta bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kansu, sakamakon karar da gwamnatin tarayya ta shigar a gabanta.

Da yake mayar da martini kan lamarin lokacin taron ‘yan jarida a Abuja, dan majalisan dattawa mai makiltar Kogi ta yamma, Sunday Karimi ya bayyana cewa majalisa za ta tabbatar da cewa gwamnonin jihohi sun yi bara’a ga hukuncin kotun koli tare da gyara kundin tsarin mulki domin shigar da sabbin batutuwa.

ADVERTISEMENT
  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Digirin Bogi A Nijeriya – Minista
  • Tsadar Rayuwa: ‘Yan Majalisa Sun Rage Albashinsu Da Kashi 50 Cikin 100

Dan jamalisar ya ce, “Cikin abubuwan da za a gyara akwai mayar da gudanar da zabe karkashin hukumar zabe ta kasa daga wurin hukumomin zabe na jihohi.”

Sanatan ya kara da cewa har yanzu tsugue ba ta kare ba, domin wasu gwamnonin za su kalubalanci lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

“Shugaban kasa Bola Tinubu ya sakar wa bangaren shari’a mara wajen gudanar da wannan shari’a ba tare da la’akari da cewa yana zangon farko ne na shugabancin kasa wanda zai so ya kara yin zago na biyu a 2027,” in ji Karimi.

Kazalika, dan majalisan dattawa mai wakiltar Delta ta tsakiya, Okakuro Ede Dafinone ya ce bisa samun wannan ci gaban, za a yi wa kundin tsarin mulkin Nijeriya kwaskwarima, domin bai wa INEC daman gudanar da zaben kananan hukumomi kai tsaye a hukumance.

Ya ce “Abun takaici ne a ce mutane ba sa amfana da tsarin dimokuradiyyarmu sakamakon yadda gwamnoni suka ki sakar wa kananan hukumomi mara wajen bari a zabi kansiloli da shugaban kananan hukumomi.

“Gwamnoninmu ne suke zaben shugabannin kananan hukumomi da kansu a jihohinsu. Idan a ce INEC za ta gudanar da zabe kamar yadda gwamnoni suke zaben kananan hukumomin, da yawa daga cikinsu ba za su zama gwamnoni ba a yau.

“Ina tunanin wanna shi ne karo na farko a tarihin kasar nan da kuma dimokuradiyyarmu, za mu yi watsi da bambancin siyasa wajen hada kai mu yi aiki tare domin gyara wani bangare na tsarin mulkinmu wajen ceto kananan hukumomi daga hannun gwamnoninmu.

“Ina yaba wa kokarin Shugaban kasa Bola Tinubu bisa wannan tunani na tabbatar da ‘yancin kananan hukumomin kasar nan.

“Za mu yi aiki da tsarin dimokuradiyya a matakin kananan hukumomi wajen tabbatar da INEC ta gudanar da zaben kananan hukumomi a fadin kasar nan, domin bai wa mutanenmu damar shiga harkokin gwamnatin dimokuradiyya.”

Sanata Dafinone siffanta zaben kananan hukumomin da ya gudana a Jihar Delta a matsayin abun kunya ga tsarin dimokuradiyya.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.