Yayin da mambobin Ƙungiyar Ma’aikatan Shari’a ta Najeriya (JUSUN) suka fara yajin aiki a ranar Litinin, lauyoyi da masu neman shari’a sun cirko-cirko a gaban kotuna da dama a birnin tarayya Abuja.
A harabar kotun da ke kan titn Shehu Shagari, an rufe dukkan kofofin shiga tare da kulle duka ofisoshi da sauran sassan ginin koton wanda wannan matakin ya shafi kotuna masu muhimmanci da dama a birnin, ciki har da Kotun Ɗaukaka Ƙara da kuma Babbar Kotun Tarayya da ke harabar ginin.
- Masu Garkuwa Sun Kashe Ɗan Alƙaliya, Sun Nemi Miliyan 300 Kafin Sako Ragowar Ƴaƴan
- Gwamnan Bauchi Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Banga A Alkaleri
Yajin aikin ya biyo bayan umarnin da Ƙungiyar JUSUN ta Ƙasa ta bayar, inda ta umurci shugabannin rassan ƙungiyar a jihohi da su fara aiwatar da zaman gida daga tsakar daren ranar 1 ga watan Yuni, 2025.
“Wannan umarnin ya biyo tattaunawa da dama da muka yi da hukumomin da suka dace domin ganin an biya mana bukatun mu da muka dade muna neman gwamnati da ta biya mana, amma har yanzu abin shiru” in ji wani da ga cikin shugabannin kungiyar a Abuja
Daga Cikin bukutun kugiyar dai akwai; binyansu albashin watanni biyar da suke bi a tsarin aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000, da kuma ƙarin albashi da kaso 25 zuwa 35 cikin ɗari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp