ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Garkuwa Sun Kashe Ɗan Alƙaliya, Sun Nemi Miliyan 300 Kafin Sako Ragowar Ƴaƴan

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Garkuwa

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe ɗaya daga cikin ƴaƴan Janet Galadima, wata alkaliyar kotu, a lokacin da suka yi garkuwa da su a Kaduna.

Masu garkuwa da mutanen na neman a biya su kudin fansa Naira miliyan ₦300m domin sako sauran ƴaƴanta. An yi garkuwa da Alƙaliyar da ƴaƴanta huɗu a gidansu yayin da mijinta Dakta Musa Gimba Dutse ya tafi wani taron a Kano.

An kashe babban ɗan, Victor a ranar 2 ga Yuli, 2024, a wani yunƙuri na matsawa dangin su biya kuɗin fansa.

ADVERTISEMENT
  • Wata Sabuwa: KEDCO Ta Yanke Wutar Jami’ar Dangote Da Ke Kano 
  • Rikicin Masarautar Kano: NNPP Ta Nesanta Kanta Daga Umarnin Kwankwaso Ga Ƴan Majalisa 

Da take mayar da martani kan lamarin, shugabar kamfanin House of Justice, Gloria Mabeiam Ballason, ta yi Allah-wadai da garkuwar da aka yi da kuma kisan, inda ta bayyana lamarin a matsayin abin ban tsoro tare da yin kira da a gaggauta samar da kayan aiki don kubutar da waɗanda aka kama tare da gurfanar da waɗanda suka aikata laifin a gaban kuliya.

Ita ma ƙungiyar likitocin Nijeriya reshen jihar ta nuna rashin jin dadin ta, inda jami’in hulɗa da jama’a na ƙungiyar, Dakta Shu’aibu Joga, ya yi kira ga hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don ganin an sako iyalan da kuma magance matsalar sace-sacen mutane a jihar.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Ƙungiyar ta bayyana buƙatar gudanar da taron gaggawa da kuma taron manema labarai domin jan hankalin hukumomi da su ƙara ƙaimi wajen kubutar da waɗanda lamarin ya rutsa da su da sauran mutanen da aka sace ciki har da wani likita da aka yi garkuwa da su watanni shida da suka wuce. Sun kuma yi kira da a kwantar da hankula tare da yin taka-tsan-tsan a tsakanin mambobinsu yayin da suke tattaunawa da jami’an tsaro domin tunkarar barazanar da ake fuskanta.

Garkuwa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
  • Abubakar Sulaiman
    Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila
  • Abubakar Sulaiman
    Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Tinubu Zai Halarci  Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma'a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

LABARAI MASU NASABA

Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Garkuwa

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.