• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alfanun Da Ke Tattare Da Sabon Tsarin Cire Kudi Na CBN – Sanusi

byYusuf Shuaibu
3 years ago
Sanusi

Tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Sanusi Lamido Sanusi ya bayyana cewa sabon tsarin da CBN ya bullo da shi na kayyade cire kudi yana da alfanu mai yawan gaske.

Ya ce tsarin ya dade tun a 2012 lokacion da yake gwamanan babban bankin suka so bullo da shi, ya ce a yanzu CBN ya ci gaba daga inda ya tsaya.

  • Abubuwan Lura Guda 6 Game Da Sabbin Dokokin CBN Na Mu’amalar Kudi

Ya ce, “Tsarin takaita cire kudade ya samo asali ne tun a 2012 lokacin da nake gwamnan CBN, inda aka fara da Jihar Legas sannan ya watsu har zuwa jihohi guda biyar. Bayanan da muka samu a wancen lokaci, duniya tana bunkasa wanda take hana mutane rike tsabar kudi tare da samar da sabon tsarin takaita kudade wajen gudanar da hada-hadar kasuwanci.

“Da farko mutane sun kalubalanci tsarin, amma daga baya sun amince da shi tare da fara yin amfani da mabanbantan tsarin biyan kudade a wuraren cin abinci da shaguna da sauran wurare,” in ji shi.

Ya kara da cewa daya daga cikin muhimmancin dokar kayyade kudade shi ne, zai hana yin magudin siyan kuri’u, sannan ya gargadi ‘yan Nijeriya su manta da ‘yan siyasan da suke korafi kan wannan doka domin su zai fi shafa sakamakon amfani da kudade da suke yi wajen sayan kuri’u.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

“Ina shawartar mutane su kuda da ‘yan siyasan da suke kalubalantar tsarin dokar kayyade cire kudadde, domin su za su fi cutuwa da tsarin. Suna kwashe shekaru hudu a kan mukami ba tare da sun iya sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ba, sannan daga baya su riko makudan kudade da suke tunanin za su yi amfani da su wajen bai wa jami’an tsaro da jami’an zabe ci hanci.

“Tsarin zai kuntata wa ‘yan siyasan da ke kokarin bai wa jami’an tsaro da jami’an zabe cin hanci, dole mutum ya saka kudaden a asusunsa na kashin kai wanda kuma za a iya bincikawa. Domin haka, ina kira ga mutane su rungumi tsarin hannu bibbiyu a matsayin hanyar tsaftace dimokuradiyya da kuma hana ‘yan siyasa yin murdiya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Buhari Zai Kaddamar Da Sabbin Takardun Kudi A Taron Majalisar Zartwar Ta Kasa Ranar Laraba

Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version