• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ali Nuhu: Shekara 50 Masu Dauke Manyan Nasarori

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Ali Nuhu

Ali Nuhu Muhammad ko kuma Sarki Ali Nuhu kamar yadda ake kiransa a masana’antar Kannywood inda ya shafe shekaru fiye da 25 yana nuna bajintarsa ta wasan kwaikwayo, ya zamo wani ginshiki a masana’antar Kannywood tsawon wadannan shekaru.

Ali Nuhu wanda ya fara harkar fim a shekarunsa na kuruciya bayan da ya kammala aikinsa na bautar kasa,ya zama daya daga cikin jaruman da tauraruwarsa ta dade tana haskawa a masana’antar, daga jarumi zuwa mai daukar nauyi kuma zuwa mai bayar da umarni a masana’antar wanda yanzu haka shi ne shugaban hukumar Fina Finai ta Nijeriya mukamin da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bashi duba da kwarewa da gogewarsa a harkar.

  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma
  • Al’adar Tashe A Kasar Hausa

Ali Nuhu Mohammed an haife shi a ranar 15 ga watan Maris a shekarar 1974,ya auri Maimuna Garba a shekarar 2003 inda suka haifi ‘ya’ya 2 Ahmed da Fatima.

Ali Nuhu dan wasan kwaikwayo ne da ya yi shura a ciki da wajen Nijeriya wanda yanzu haka shi ne manajan darakta na hukumar Fina-Finan Nijeriya wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada shi ranar Juma’a 12 ga Janairu 2024.

Kafin nadin nasa, fitaccen dan wasan kwaikwayo ne kuma darakta inda yake fitowa a fina-finan Hausa da na turanci, sannan kuma ana kiransa da Sarkin Kannywood ko kuma Sarki Ali.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Ali Nuhu ya fito a fina-finan Nollywood da na Kannywood sama da 500, kuma ya samu lambobin yabo da dama, ana kallon Ali Nuhu a matsayin daya daga cikin fitattun jaruman fina-finan Hausa a tarihi, kuma an bayyana shi a matsayin wanda ya fi samun nasara a fim din Hausa.

Ali ya fara fitowa a fim din Abin Sirri ne a shekarar 1999,ya kuma shahara sanadiyar rawar da ya taka a fim din Sangaya, wanda ya zama daya daga cikin fina-finan Hausa da suka fi samun kudi a lokacin, ya haskaka a fina-finai da dama, da suka hada da Sai Watarana,Ali,Alaka da sauransu shi ya samu kyautar Gwarzon Jarumi a wajen bayar da lambar yabo ta African Mobie Academy Awards (2007).

A shekarar 2019 Ali Nuhu ya yi bikin cika shekaru 20 a harkar nishadantarwa inda ya fito a fina-finai kusan dari biyar, yana daya daga cikin fitattun jaruman fina-finan Hausa, ya kan fito a jerin fitattun mutane,masu tasiri a Nijeriya.

Ya kasance yana fitowa a kai a kai cikin manyan mutane goma daga cikin 100 mafiya tasiri a Nijeriya ya kuma kasance jakadan kamfen na gwamnati da na sa-kai da suka hada da Globacom,YALE da sauran su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Next Post
Shugaban Kwamitin ECOWAS: Sin Ta Taka Muhimmiyar Rawa Ga Ci Gaban Yankunan Yammacin Afirka

Shugaban Kwamitin ECOWAS: Sin Ta Taka Muhimmiyar Rawa Ga Ci Gaban Yankunan Yammacin Afirka

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.