• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ali Nuhu: Shekara 50 Masu Dauke Manyan Nasarori

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
Ali Nuhu: Shekara 50 Masu Dauke Manyan Nasarori
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ali Nuhu Muhammad ko kuma Sarki Ali Nuhu kamar yadda ake kiransa a masana’antar Kannywood inda ya shafe shekaru fiye da 25 yana nuna bajintarsa ta wasan kwaikwayo, ya zamo wani ginshiki a masana’antar Kannywood tsawon wadannan shekaru.

Ali Nuhu wanda ya fara harkar fim a shekarunsa na kuruciya bayan da ya kammala aikinsa na bautar kasa,ya zama daya daga cikin jaruman da tauraruwarsa ta dade tana haskawa a masana’antar, daga jarumi zuwa mai daukar nauyi kuma zuwa mai bayar da umarni a masana’antar wanda yanzu haka shi ne shugaban hukumar Fina Finai ta Nijeriya mukamin da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bashi duba da kwarewa da gogewarsa a harkar.

  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma
  • Al’adar Tashe A Kasar Hausa

Ali Nuhu Mohammed an haife shi a ranar 15 ga watan Maris a shekarar 1974,ya auri Maimuna Garba a shekarar 2003 inda suka haifi ‘ya’ya 2 Ahmed da Fatima.

Ali Nuhu dan wasan kwaikwayo ne da ya yi shura a ciki da wajen Nijeriya wanda yanzu haka shi ne manajan darakta na hukumar Fina-Finan Nijeriya wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada shi ranar Juma’a 12 ga Janairu 2024.

Kafin nadin nasa, fitaccen dan wasan kwaikwayo ne kuma darakta inda yake fitowa a fina-finan Hausa da na turanci, sannan kuma ana kiransa da Sarkin Kannywood ko kuma Sarki Ali.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ali Nuhu ya fito a fina-finan Nollywood da na Kannywood sama da 500, kuma ya samu lambobin yabo da dama, ana kallon Ali Nuhu a matsayin daya daga cikin fitattun jaruman fina-finan Hausa a tarihi, kuma an bayyana shi a matsayin wanda ya fi samun nasara a fim din Hausa.

Ali ya fara fitowa a fim din Abin Sirri ne a shekarar 1999,ya kuma shahara sanadiyar rawar da ya taka a fim din Sangaya, wanda ya zama daya daga cikin fina-finan Hausa da suka fi samun kudi a lokacin, ya haskaka a fina-finai da dama, da suka hada da Sai Watarana,Ali,Alaka da sauransu shi ya samu kyautar Gwarzon Jarumi a wajen bayar da lambar yabo ta African Mobie Academy Awards (2007).

A shekarar 2019 Ali Nuhu ya yi bikin cika shekaru 20 a harkar nishadantarwa inda ya fito a fina-finai kusan dari biyar, yana daya daga cikin fitattun jaruman fina-finan Hausa, ya kan fito a jerin fitattun mutane,masu tasiri a Nijeriya.

Ya kasance yana fitowa a kai a kai cikin manyan mutane goma daga cikin 100 mafiya tasiri a Nijeriya ya kuma kasance jakadan kamfen na gwamnati da na sa-kai da suka hada da Globacom,YALE da sauran su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Angola: Sin Tana Hadin Gwiwa Tare Da Kasashen Afirka Maimakon Mulkin Mallaka

Next Post

Shugaban Kwamitin ECOWAS: Sin Ta Taka Muhimmiyar Rawa Ga Ci Gaban Yankunan Yammacin Afirka

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

5 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

2 weeks ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

3 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

4 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Shugaban Kwamitin ECOWAS: Sin Ta Taka Muhimmiyar Rawa Ga Ci Gaban Yankunan Yammacin Afirka

Shugaban Kwamitin ECOWAS: Sin Ta Taka Muhimmiyar Rawa Ga Ci Gaban Yankunan Yammacin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.