• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ali Nuhu: Shekara 50 Masu Dauke Manyan Nasarori

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
Ali Nuhu: Shekara 50 Masu Dauke Manyan Nasarori
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ali Nuhu Muhammad ko kuma Sarki Ali Nuhu kamar yadda ake kiransa a masana’antar Kannywood inda ya shafe shekaru fiye da 25 yana nuna bajintarsa ta wasan kwaikwayo, ya zamo wani ginshiki a masana’antar Kannywood tsawon wadannan shekaru.

Ali Nuhu wanda ya fara harkar fim a shekarunsa na kuruciya bayan da ya kammala aikinsa na bautar kasa,ya zama daya daga cikin jaruman da tauraruwarsa ta dade tana haskawa a masana’antar, daga jarumi zuwa mai daukar nauyi kuma zuwa mai bayar da umarni a masana’antar wanda yanzu haka shi ne shugaban hukumar Fina Finai ta Nijeriya mukamin da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bashi duba da kwarewa da gogewarsa a harkar.

  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma
  • Al’adar Tashe A Kasar Hausa

Ali Nuhu Mohammed an haife shi a ranar 15 ga watan Maris a shekarar 1974,ya auri Maimuna Garba a shekarar 2003 inda suka haifi ‘ya’ya 2 Ahmed da Fatima.

Ali Nuhu dan wasan kwaikwayo ne da ya yi shura a ciki da wajen Nijeriya wanda yanzu haka shi ne manajan darakta na hukumar Fina-Finan Nijeriya wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada shi ranar Juma’a 12 ga Janairu 2024.

Kafin nadin nasa, fitaccen dan wasan kwaikwayo ne kuma darakta inda yake fitowa a fina-finan Hausa da na turanci, sannan kuma ana kiransa da Sarkin Kannywood ko kuma Sarki Ali.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ali Nuhu ya fito a fina-finan Nollywood da na Kannywood sama da 500, kuma ya samu lambobin yabo da dama, ana kallon Ali Nuhu a matsayin daya daga cikin fitattun jaruman fina-finan Hausa a tarihi, kuma an bayyana shi a matsayin wanda ya fi samun nasara a fim din Hausa.

Ali ya fara fitowa a fim din Abin Sirri ne a shekarar 1999,ya kuma shahara sanadiyar rawar da ya taka a fim din Sangaya, wanda ya zama daya daga cikin fina-finan Hausa da suka fi samun kudi a lokacin, ya haskaka a fina-finai da dama, da suka hada da Sai Watarana,Ali,Alaka da sauransu shi ya samu kyautar Gwarzon Jarumi a wajen bayar da lambar yabo ta African Mobie Academy Awards (2007).

A shekarar 2019 Ali Nuhu ya yi bikin cika shekaru 20 a harkar nishadantarwa inda ya fito a fina-finai kusan dari biyar, yana daya daga cikin fitattun jaruman fina-finan Hausa, ya kan fito a jerin fitattun mutane,masu tasiri a Nijeriya.

Ya kasance yana fitowa a kai a kai cikin manyan mutane goma daga cikin 100 mafiya tasiri a Nijeriya ya kuma kasance jakadan kamfen na gwamnati da na sa-kai da suka hada da Globacom,YALE da sauran su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Angola: Sin Tana Hadin Gwiwa Tare Da Kasashen Afirka Maimakon Mulkin Mallaka

Next Post

Shugaban Kwamitin ECOWAS: Sin Ta Taka Muhimmiyar Rawa Ga Ci Gaban Yankunan Yammacin Afirka

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

6 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

3 weeks ago
Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

3 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 weeks ago
Next Post
Shugaban Kwamitin ECOWAS: Sin Ta Taka Muhimmiyar Rawa Ga Ci Gaban Yankunan Yammacin Afirka

Shugaban Kwamitin ECOWAS: Sin Ta Taka Muhimmiyar Rawa Ga Ci Gaban Yankunan Yammacin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.