• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alkawuran Zuba Jarin Dala Biliyan 14 Da Rawar Da NIS Za Ta Taka 

by CIS James Sunday
2 years ago
in Labarai
0
NIS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba sabon labari ba ne cewa Nijeriya ta samu nasarar janyo hankalin kamfanonin kasar Indiya domin zuba hannun jari na biliyoyin dala. Yana da kyau mu dan bi tare da nazartar irin rawar da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta za ta taka wajen cimma wannan nasarar da ma wasu da dama.

Ba kamar a baya ba, Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da tawagarsa ta kwararru daga Nijeriya sun samu nasarar aza tubalin ci gaba ta siyasa da tattalin arziki inda suka samu wasu masu zuba jari daga kasar da suka sha alwashin zuba Dala Biliyan 14 a bangaren harkokin bunkasa tattalin arziki.

  • NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

A karkashin wannan nasara da Nijeriya ta samu akwai abubuwa da dama da suka shafi Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS). Saboda NIS ita ce hukuma ta farko da ake fara riska da zarar an shigo cikin kasa, da kula da bangaren samar da izinin shigo ga ‘yan kasashen waje (Biza) da kuma sahalewa ga masu shigo cikin kasa, da masu son zama da kuma masu kawo ayyuka a bangarori daban-daban na bunkasar tattalin arziki.

Kazalika, NIS na sanya ido da bibiyar bakin da aka amince su kasance a cikin kasa, da kula da izinin masu gudanar da harkokin kasuwanci, sannan tana da dabarun inganta bayar da Biza ga manyan masu zuba hannun jari, da saukaka wa masu gudanar da kasuwanci harkokinsu da masu ruwa da tsaki da sabbin masu zuba hannun jari inda suke samun aiki mai nagarta cikin sauki daga hukumar. Wannan yakan ba su kwarin guiwa da damar zabar Nijeriya a matsayin kasar da za su zo zuba hannun jarinsu, da tabbatar da shimfidar fuska ga baki, masu zuwa yawon bude ido da sauran fannonin da ke kyautata harkokin tattalin arziki.

Domin kyautata harkokin tattalin arzikin Nijeriya bisa sabon shirin bunkasa arzikin kasa da na yi wa lakabi da “Tinubunomics”, akwai bukatar kara kyautata dangantakar aiki mai ma’ana a tsakanin hukumar NIS, da takwarorinta irin su Hukumar Hana Fasa Kwauri (Kwastam), da Hukumar Kula da Al’amuran Shige da Ficen Teku ta NIMASA, da Kamfanin Mai na Kasa (NNPC), da Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama, da jami’an kiwon lafiya, da na NIPC, da Bankin Ba Da Lamunin Kasuwancin Shige da Fice (NEDIM), da sauran bankunan kasuwanci, da bankunan masana’antu da kuma dokokin da suke gudanar da harkokin zuba jari a Nijeriya, da duba yarjejeniyar da suka shafi aiki da kwararru ‘yan kasashen waje a bangaren kula da bakin waje da kamfanonin da suke musu aiki da dai sauran harkoki da NIS ke zama daya daga cikin masu ruwa da tsaki.

Labarai Masu Nasaba

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

Alllah ya albarkaci Nijeriya da dumbin abubuwan da za a iya zuba musu jari da kuma albarkatun kasa masu tarin yawa. Yanzu haka kasar ta yi nisa wajen kawo gyara mai ma’ana a bangarorin zuba jari da kuma saukaka hanyoyin daukar dawainiyar masu zuwa cikin kasar domin kawo ci gaba.

Bayan haka, ya zama wajibi masu kula da harkokin tattalin arziki su kara maida hankali wajen ganin an rage yawan dogaro da ‘yan kasashen waje ta fuskar gudanar da aikace-aikace da kara ingantawa da muhimmanta amfani da albarkatun kasa da muke da su, da lalubo bakin zaren kara habaka yadda ake mayar da bola zuwa abubuwan amfani. Sannan yana da matukar kyau a kara inganta dokokin harkokin ma’adinai da kuma sanya ido kan filayen da ake bai wa kamfanonin kasashen waje.

Har ila yau, dole ne ma’aikatu da rassansu da sauran hukumomi su tabbatar da yin tsari mai inganci da zai kai ga kyautata tattalin arziki da ba da tasu gudunmawar a wannan fannin. Kana a bi sannu a hankali wajen aiwatar da tsare-tsare da manufofin gwamnati, da rage yawan bata lokaci da tsadar kayayyaki a kasuwannin Nijeriya da ke hana masu zuba jari da dama zama a Nijeriya wanda suke wucewa zuwa kasashen Ghana da sauran kasashen Afirka domin zuba hannun jari ko sayar da kayansu. Akwai bukatar a duba wannan matsalar domin yin kwaskwarima kwarai da gaske.

NIS na da gagarumar rawar da za ta ci gaba da takawa wajen kara janyo kamfanoni domin su zo su zuba hannun jari, da aiki da kwararru, da ‘yan kasuwa, da saukaka kasuwanci da kuma mayar da hankali wajen inganta ayyukan da za su taimaka wajen kara nuna wa masu zuba jari cewar Nijeriya ta cancanta a yi hulda da ita.

CIS James Sunday, shi ne Kwanturolan Hukumar Kula Da Shige Da Fice (NIS) A Jihar Ribas


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Masu Kashe Kansu Da Masu Yunkurin Haka A Nijeriya

Next Post

Na’urorin Tattara Wutar Lantarki Na TCN A Birnin Kebbi Sun Fashe

Related

Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike
Manyan Labarai

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

1 hour ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

2 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

12 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara
Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

13 hours ago
NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya
Labarai

NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

14 hours ago
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

16 hours ago
Next Post
Na’urorin Tattara Wutar Lantarki Na TCN A Birnin Kebbi Sun Fashe

Na'urorin Tattara Wutar Lantarki Na TCN A Birnin Kebbi Sun Fashe

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

September 1, 2025
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

September 1, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

September 1, 2025
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.