Majalisar zartaswa ta Jam’iyar Adawa ta Labour party (LP) a karkashin jagorancin Sanata Nenadi Usman da Sakataren Jam’iyar, Sanata Darlington Nwokwocha, ta kafa wani kwamitin horo, karkashin jagorancin Sanata Ireti Kingibe da wasu mambobi hudu domin su binciki Almundahana da zagon Kasa Ga Jam’iyar Wanda ake zargin tsohon Shugaban Jam’iyar Julius Abure da aikatawa.
Hakan ya biyon bayan wani taron manema labarai, Wanda Shugaban Jam’iyar (mai rikon kwarya) na Kasa, Sanata Nenadi Usman ta yi a Abuja.
Shugaba Xi Ya Isa Moscow Domin Fara Ziyarar Aiki A Rasha
An dai bai wa kwamitin wa’adin sati uku domin su gabatar da rahoton su. Ita dai Sanata Ireti Wanda ke wakiltar Birnin tarraya Abuja, itace za ta Shugabanci kwamitin sai kuma aka nada Peter Ameh a matsayin sakataren kwamitin.
Har ila yau, kwamitin zai bada shawara akan hukuncin da Jam’iyar za ta dauka Idan har aka sami wanda ake zargi da laifin almundahana da kuma zagon Kasa ga LP a lokacin da yake Shugabantar jam’iyar.
Sanata Usman ta zargi Abure da mukarrabansa da aikata laifufuka dake janyo rabuwar Kai ga ‘ya’yan Jamiyar tare da batanci da haddasa rikici.
Sanata Usman ta Kara da cewa, Abure yana aikata laifufuka wanda suke kalubalantar mutunci Jam’iyar da kuma yin karo da manufofin dimokuradiyya. Don haka, majalisar zartaswa ta Jam’iyar ta dauki matakin kaddamar da bincike kan wannan munanan halayya.
Bugu da Kari Sanata Nenadi Usman tace majalisar zantaswa na Jamiyar Labour bayan dogon nazari akan hukuncin da kotun koli ta Kasa ta yi na ranar 4 ga watan Afrilun 2025, Jam’iyar ta nuna matukar damuwarta akan Yadda Julius Abure yake amfani da sunan shi a matsayin Shugaban Jam’iyar bayan wa’adin jagorancin shi ya cika.
Ta ce, abubuwan da Julius Abure yake yi ya sabawa dokar Kasa kuma ya ci mutuncin Jamiyar. A sabo da haka ne tace kundin tsarin mulkin Jamiyar na shekarar 2019 (Wanda aka yi wa Kwaskwarima) ya Basu damar daukan kwararan matakai da hukunci akan Julius Abure.
Daga bisani, Sanata Nenadi Usman ta nuna rashin amincewarta akan Yadda Julius Abure yake cin mutunci jagoran jam’iyar Labour na Kasa, Peter Obi da Gwamna Alex Otti. Tace Abure da mukarabansa wadanda wa’adinsu ya kare, basu da hurumin magana da yawun Jam’iyar kuma baza su iya dakatar da Gwamnan ba ko wani mamban Jamiyar.
Ta kuma shaidawa ‘Yan Nijeriya cewa, Jam’iyar ta sanar da Hukumar Zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) akan shirye-shiryenta na gudanar da zabuka a matakai daban-daban tare da gudanar da babban taron Jam’iyar na kasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp