ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

by Sadiq
8 months ago
Tinubu

Fadar Shugaban Ƙasa, ta ce babu wani ɗan siyasa a Nijeriya da zai iya ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaɓen shekarar 2027.

Mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala ne, ya bayyana hakan a ranar Talata a Abuja yayin wani taro da aka gudanar tare da ƙungiyoyi  sama da 100 masu goyon bayan Tinubu.

  • Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu
  • Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Taron mai taken “Tattaunawa da Mai Magana da Yawun Shugaban Ƙasa,” an shirya shi ne domin bunƙasa haɗin kai tsakanin Fadar Shugaban Ƙasa da magoya bayan Tinubu kafin zaɓen 2027.

ADVERTISEMENT

Bwala, ya ce manufar taron ita ce a yaba wa ƙungiyoyi da kuma ƙarfafa musu gwiwa su ci gaba da aikin da suke yi.

“Mun zo ne don yi godiya ga ƙungiyoyin da ke goyon bayan shugaban ƙasa bisa irin kokarin da suke yi, tare da roƙonsu su ƙara jajircewa saboda son ƙasa da kuma son Shugaban Ƙasa,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ya ce manufofi da sauye-sauyen da Shugaba Tinubu ya aiwatar cikin shekaru biyu da suka gabata sun ƙara wa jama’a ƙwarin gwiwa game da tattalin arziƙin ƙasa da tafiyar da gwamnati, abin da ya sa zai yi wuya a kayar da shi a 2027.

“Babu wani ɗan siyasa a yau da zai iya ƙalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Muna tafiya da ‘sabon fata’ zuwa ‘farfafowa,’ kuma wannan farfaɗowar dole ne ta bayyana a rayuwar talakawa,” in ji Bwala.

Ya ƙara da cewa shugabannin ƙungiyoyi daga dukkanin shiyyoyi shida na ƙasar nan sun halarci taron, ciki har da wasu da suka zo daga Biritaniya.

Bwala, ya bayyana cewa taron ba yaƙin neman zaɓe ba ne, amma wata dama ce don gina kyakkyawar alaƙa tsakanin gwamnati da abokan hulɗa na ƙasa.

“Wasu mutane suna jiran lokacin zaɓe kafin su nemi ƙungiyoyi, amma wannan ba daidai ba ne. Ba kayan aiki ba ne, abokan tafiya ne, dole su kasance cikin abin da gwamnati ke yi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa irin waɗannan taruka za a shirya su a Biritaniya, Amurka da Kanada don tattaunawa da ’yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje da kuma yaɗa bayanai game da nasarorin gwamnatin Tinubu.

Bwala, ya bayyana cewa Fadar Shugaban Ƙasa tana shirin gudanar da babban taron tattaunawa a watan Nuwamba, inda dukkanin ƙungiyoyi za su haɗu domin nazarin dabarunsu da kuma kimanta yadda gwamnati ke aiki.

Ya ce sauye-sauyen tattalin arziƙi da gwamnatin Tinubu ta fara aiwatarwa sun fara bayar da sakamako a fannoni daban-daban kamar makamashi, noma, ayyukan gina ƙasa da samar da ayyukan yi.

“Mun riga mun fara ganin sakamako. Idan muka je fagen aiki, za mu ga ci gaba a bangaren tattalin arziƙi, tsaro, ilimi da noma. Waɗannan ƙungiyoyi za su ci gaba da yaɗa wannan saƙo,” in ji shi.

Shi ma tsohon ɗan majalisa, Hon. Ehiozuwa Johnson Agbonayinma, wanda ya halarci taron, ya yaba wa jagorancin Tinubu.

“Ko mutum ya so ko ya ƙi, Shugaban Ƙasa zai sake lashe zaɓe a 2027. Ba mu kai inda muke so ba tukuna, amma muna cimma nasara. Shugaban Ƙasa na yin duk abin da zai yi don kawo ci gaba,” in ji shi.

Agbonayinma, ya kuma yaba da cire tallafin man fetur, yana mai cewa hakan ya ba da damar a saki maƙudan kuɗaɗe don jihohi su inganta ci gaban al’umma a matakin ƙasa.

Dukkanin masu jawabin sun buƙaci ƙungiyoyin su ci gaba da yaɗa manufofin gwamnati da kuma tabbatar da haɗin kai tsakanin yankuna da jam’iyyu.

Bwala, ya kuma buƙaci magoya bayan Tinubu su ci gaba da nuna goyon baya da ƙauna ga Shugaban Ƙasa.

“Shugaba Tinubu ya yi abin da ya cancanci ba kawai goyon bayan jama’a ba, har ma da soyayya da jajircewarsu don ci gaba da abin da gwamnatinsa ta fara,” in ji shi.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.