• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Da Birtaniya Da Australiya Sun Ci Gaba Da Shirinsu Kan Jirgin Karkashin Ruwa Mai Amfani Da Makamashin Nukiliya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Da Birtaniya Da Australiya Sun Ci Gaba Da Shirinsu Kan Jirgin Karkashin Ruwa Mai Amfani Da Makamashin Nukiliya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 13 ga wata, shugabannin kasashen Amurka, Birtaniya da Australiya sun gana tare da sanar da shirinsu na samar wa Australiya jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya.

Sanarwar hadin gwiwar da kasashen 3 suka bayar ta ce, Amurka za ta sayar wa Australiya jiragen karkashin ruwa masu amfani da makamashin nukiliya samfurin Virginia guda 3 a farkon shekaru 2030, daga baya kuma ta kara sayar mata jirage 2 na daban. Haka kuma kasashen 3 sun shirya nazarin wani sabon nau’in jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, bisa tushen fasahohin Amurka da Birtaniya.

  • Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Yadda Amurka Ta Kara Sanyawa Kamfanonin Sin Takunkumi

A cewar wani jami’in Australiya, za a kammala shirin baki daya a shekarar 2055, wanda za a kashe dalar Amurka biliyan 245 wajen aiwatarwa.

Kwanaki da dama kafin kasashen 3 su sanar da shirinsu, an gudanar da taron hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta IAEA na watan Maris a birnin Vienna, inda sakamakon kokarin da kasar Sin ta yi, an tattauna tare da nazarin batun hadin gwiwar da ke tsakanin Amurka da Birtaniya da Australiya kan jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, tsakanin mambobin hukumar karo na 7 a jere. Wasu kasashe sun nuna adawa kan hadin gwiwar kasashen 3.

Amma kasashen 3 sun kau da kai daga damuwar kasa da kasa, sun ci gaba da sanar da shirin nasu, a yunkurin daukar matakin kashin kai, a maimakon cimma daidaito tsakanin bangarori daban daban, sun kara fadawa hanya mai hadari wadda kuma ba ta dace ba.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Muddin aka aiwatar da shirinsu a zahiri, to, tabbas za a illata zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Asiya da tekun Fasifik, da yi wa tsarin hana yaduwar nukiliya na kasa da kasa barna, da sa kaimi kan yin takarar makamai, matakin da zai haifar da illoli masu dimbin yawa a nan gaba.

Hakika hadin gwiwar da ke tsakanin Amurka, Birtaniya da Australiya kan jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, ba su ukun kadai ta shafa ba, tana da nasaba da muradun dukkan kasashe mambobin IAEA. Don haka, kamata ya yi mambobin IAEA su tattauna su kuma tsai da kuduri tare. Kafin a cimma daidaito kan wannan batu, bai kamata ba kasashen 3 su kaddamar da shirinsu. (Tasallah Yuan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Kudi: Ka Sallami Emefiele Daga Aiki -Hadimin Tinubu Ga Buhari

Next Post

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Dage Kidayar Jama’a Zuwa Watan Mayun 2023

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

1 hour ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

3 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

4 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

5 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

22 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

23 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Dage Kidayar Jama’a Zuwa Watan Mayun 2023

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Dage Kidayar Jama'a Zuwa Watan Mayun 2023

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.