• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Da Birtaniya Da Australiya Sun Ci Gaba Da Shirinsu Kan Jirgin Karkashin Ruwa Mai Amfani Da Makamashin Nukiliya

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Ranar 13 ga wata, shugabannin kasashen Amurka, Birtaniya da Australiya sun gana tare da sanar da shirinsu na samar wa Australiya jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya.

Sanarwar hadin gwiwar da kasashen 3 suka bayar ta ce, Amurka za ta sayar wa Australiya jiragen karkashin ruwa masu amfani da makamashin nukiliya samfurin Virginia guda 3 a farkon shekaru 2030, daga baya kuma ta kara sayar mata jirage 2 na daban. Haka kuma kasashen 3 sun shirya nazarin wani sabon nau’in jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, bisa tushen fasahohin Amurka da Birtaniya.

  • Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Yadda Amurka Ta Kara Sanyawa Kamfanonin Sin Takunkumi

A cewar wani jami’in Australiya, za a kammala shirin baki daya a shekarar 2055, wanda za a kashe dalar Amurka biliyan 245 wajen aiwatarwa.

Kwanaki da dama kafin kasashen 3 su sanar da shirinsu, an gudanar da taron hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta IAEA na watan Maris a birnin Vienna, inda sakamakon kokarin da kasar Sin ta yi, an tattauna tare da nazarin batun hadin gwiwar da ke tsakanin Amurka da Birtaniya da Australiya kan jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, tsakanin mambobin hukumar karo na 7 a jere. Wasu kasashe sun nuna adawa kan hadin gwiwar kasashen 3.

Amma kasashen 3 sun kau da kai daga damuwar kasa da kasa, sun ci gaba da sanar da shirin nasu, a yunkurin daukar matakin kashin kai, a maimakon cimma daidaito tsakanin bangarori daban daban, sun kara fadawa hanya mai hadari wadda kuma ba ta dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Muddin aka aiwatar da shirinsu a zahiri, to, tabbas za a illata zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Asiya da tekun Fasifik, da yi wa tsarin hana yaduwar nukiliya na kasa da kasa barna, da sa kaimi kan yin takarar makamai, matakin da zai haifar da illoli masu dimbin yawa a nan gaba.

Hakika hadin gwiwar da ke tsakanin Amurka, Birtaniya da Australiya kan jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, ba su ukun kadai ta shafa ba, tana da nasaba da muradun dukkan kasashe mambobin IAEA. Don haka, kamata ya yi mambobin IAEA su tattauna su kuma tsai da kuduri tare. Kafin a cimma daidaito kan wannan batu, bai kamata ba kasashen 3 su kaddamar da shirinsu. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Dage Kidayar Jama’a Zuwa Watan Mayun 2023

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Dage Kidayar Jama'a Zuwa Watan Mayun 2023

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025
Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.