ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Da Birtaniya Da Australiya Sun Ci Gaba Da Shirinsu Kan Jirgin Karkashin Ruwa Mai Amfani Da Makamashin Nukiliya

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Ranar 13 ga wata, shugabannin kasashen Amurka, Birtaniya da Australiya sun gana tare da sanar da shirinsu na samar wa Australiya jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya.

Sanarwar hadin gwiwar da kasashen 3 suka bayar ta ce, Amurka za ta sayar wa Australiya jiragen karkashin ruwa masu amfani da makamashin nukiliya samfurin Virginia guda 3 a farkon shekaru 2030, daga baya kuma ta kara sayar mata jirage 2 na daban. Haka kuma kasashen 3 sun shirya nazarin wani sabon nau’in jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, bisa tushen fasahohin Amurka da Birtaniya.

  • Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Yadda Amurka Ta Kara Sanyawa Kamfanonin Sin Takunkumi

A cewar wani jami’in Australiya, za a kammala shirin baki daya a shekarar 2055, wanda za a kashe dalar Amurka biliyan 245 wajen aiwatarwa.

ADVERTISEMENT

Kwanaki da dama kafin kasashen 3 su sanar da shirinsu, an gudanar da taron hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta IAEA na watan Maris a birnin Vienna, inda sakamakon kokarin da kasar Sin ta yi, an tattauna tare da nazarin batun hadin gwiwar da ke tsakanin Amurka da Birtaniya da Australiya kan jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, tsakanin mambobin hukumar karo na 7 a jere. Wasu kasashe sun nuna adawa kan hadin gwiwar kasashen 3.

Amma kasashen 3 sun kau da kai daga damuwar kasa da kasa, sun ci gaba da sanar da shirin nasu, a yunkurin daukar matakin kashin kai, a maimakon cimma daidaito tsakanin bangarori daban daban, sun kara fadawa hanya mai hadari wadda kuma ba ta dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Muddin aka aiwatar da shirinsu a zahiri, to, tabbas za a illata zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Asiya da tekun Fasifik, da yi wa tsarin hana yaduwar nukiliya na kasa da kasa barna, da sa kaimi kan yin takarar makamai, matakin da zai haifar da illoli masu dimbin yawa a nan gaba.

Hakika hadin gwiwar da ke tsakanin Amurka, Birtaniya da Australiya kan jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya, ba su ukun kadai ta shafa ba, tana da nasaba da muradun dukkan kasashe mambobin IAEA. Don haka, kamata ya yi mambobin IAEA su tattauna su kuma tsai da kuduri tare. Kafin a cimma daidaito kan wannan batu, bai kamata ba kasashen 3 su kaddamar da shirinsu. (Tasallah Yuan)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Dage Kidayar Jama’a Zuwa Watan Mayun 2023

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Dage Kidayar Jama'a Zuwa Watan Mayun 2023

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.