• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ita Ce Sanadin Tashin Hankalin Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Ita Ce Sanadin Tashin Hankalin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen duniya sun dade da fuskantar “juyin juya hali” da ke da hannun kasar Amurka, wadanda aka kaddamar da sunan “‘Yanci” da “Dimokuradiyya” amma domin neman juyin mulkin kasashen, musamman a kasashen Afirka da gabas ta tsakiya da gabashin Turai da tsakiyar Asiya da sauransu, juyin juya hali da aka sawa sunayen “Rose Revolution” “Orange Revolution” “Tulip Revolution” “Jasmine Revolution” da sauransu.

Sai dai a cikin wadannan al’amura, fasahohin sadarwa na taka muhimmiyar rawa. Sanin kowa ne Kasar Amurka ce ke kan gaba a duniya ta fannin fasahohin zamani, musamman ma fasahar yanar gizo da ta yayata zuwa kasashen duniya a shekarun 1980, fasahohin da suka kuma samar mata tallafi wajen kaddamar da irin wannan juyin juya hali a kasashen da ta ga dama.

  • Mirginawar Rumbun Basuka A Jihohin Kano Da Kaduna

Cibiyar tunkarar harin kumfuta ta gaggawa ta kasar Sin da kamfanin kula da tsaron yanar gizo na 360 na kasar a kwanan nan sun fitar da wani rahoto bisa binciken da suka gudanar, inda suka tona asirin hukumar leken asiri ta kasar Amurka da aka san ta da sunan CIA, ta fannin yin amfani da fasahohin yanar gizo wajen kaddamar da juyin juya hali a kasashen duniya.

Misali, Amurka ta samarwa masu kin jinin gwamnati a kasashe kamar Tunisia da Masar, wani boyayyen tsarin sadarwa domin tabbatar da matasa ‘yan adawa masu son kawo tsaiko ga gwamnati, sun gujewa bincike da sa ido daga gwamnatocinsu yayin da suke gudanar da wannan aiki.

Ko da gwamnatin kasashen sun katse harkokin sadarwa a yunkurin hana ayyukan ‘yan adawar, hukumar CIA na iya samar da hidimomin sadarwa gare su, ta yadda za su iya ci gaba da ayyukansu. Alkaluman sun shaida cewa, a shekaru sama da goma, CIA ta riga ta kifar ko kuma ta yi yunkurin kifar da wasu halastattun gwamnatoci akalla 50, tare da hura wutar rikici a kasashe da dama.
Lallai, don tayar da tashin hankali a wasu kasashe har ma da hambarar da gwamnatin kasashen, Amurka ta yi ta rura wutar rikici a kasashen, ga shi kuma matakan da suka dauka da ma fasahohin zamani da suka yi amfani da su, gaskiya sun ba mu mamaki da ma damuwa.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Duk da haka, bayan da aka kaddamar da wadannan juyin juya halin, al’ummar kasashen sun tarar da cewa, abin da ya faru ba kamar yadda aka alkawarta musu ba, a maimakon yanayin kasashensu ya kara kyautata ba, kasashen sun tsunduma cikin mawuyacin hali na tashin hankali da tabarbarewar tattalin arziki da kuma wahalar rayuwa. Yanayin da ake ciki yanzu a Libya da Iraki da Ukraine dai duk sun shaida hakan.
Sai dai kamar Amurka ba ta jin kunyar munanan ayyukanta, har ma tana ganin hakan ya zama dole, duba da yadda mai taimakawa tsohon shugaban kasar Amurka kan harkokin tsaro, John R. Bolton ya yi na’am da rawar da Amurka ta taka wajen kaddamar da juyin mulki a wasu kasashe, a yayin da yake zantawa da manema labarai, har ya ce, juyin mulki a wasu kasashe “ya zama dole wajen tabbatar da moriyar kasar Amurka”.

To, kamar yadda Mr.Bolton ya fada, Amurka ba ta damu da yanayin da kasashen za su shiga bayan “juyin juya hali” ba, abin da kawai take tunani shi ne ko wadanda za su hau karagar mulkin kasashen za su yi mata biyayya, kuma hakan na faruwa ne sakamakon yadda kullum Amurka ke mai da moriyarta a gaban kome. Domin cimma moriyarta, Amurka tana daukar iya matakan da ta ga dama wajen tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe, har da hambarar da gwamnatocinsu.

Daidai da yadda Michael Lüders, marubucin kasar Jamus ya fada, kullum Amurka tana cewa tana daga cikin masu halin kirki, wadanda ke rungumar dimokuradiyya da ‘yanci a hakkin dan Adam, “amma a hakika abin ba haka yake ba, kawai suna bin moriyarsu ne.” (Lubabatu Lei)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kankan Da Kai Na Manzon Allah (SAW) I

Next Post

Yadda Hukumar CIA Ta Amurka Ke Aikata Mugunta Wajen Satar Bayanan Sirri

Related

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

11 minutes ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

1 hour ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

18 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

19 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

20 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

21 hours ago
Next Post
Yadda Hukumar CIA Ta Amurka Ke Aikata Mugunta Wajen Satar Bayanan Sirri

Yadda Hukumar CIA Ta Amurka Ke Aikata Mugunta Wajen Satar Bayanan Sirri

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.