• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ita Ce Sanadin Tashin Hankalin Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Ita Ce Sanadin Tashin Hankalin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen duniya sun dade da fuskantar “juyin juya hali” da ke da hannun kasar Amurka, wadanda aka kaddamar da sunan “‘Yanci” da “Dimokuradiyya” amma domin neman juyin mulkin kasashen, musamman a kasashen Afirka da gabas ta tsakiya da gabashin Turai da tsakiyar Asiya da sauransu, juyin juya hali da aka sawa sunayen “Rose Revolution” “Orange Revolution” “Tulip Revolution” “Jasmine Revolution” da sauransu.

Sai dai a cikin wadannan al’amura, fasahohin sadarwa na taka muhimmiyar rawa. Sanin kowa ne Kasar Amurka ce ke kan gaba a duniya ta fannin fasahohin zamani, musamman ma fasahar yanar gizo da ta yayata zuwa kasashen duniya a shekarun 1980, fasahohin da suka kuma samar mata tallafi wajen kaddamar da irin wannan juyin juya hali a kasashen da ta ga dama.

  • Mirginawar Rumbun Basuka A Jihohin Kano Da Kaduna

Cibiyar tunkarar harin kumfuta ta gaggawa ta kasar Sin da kamfanin kula da tsaron yanar gizo na 360 na kasar a kwanan nan sun fitar da wani rahoto bisa binciken da suka gudanar, inda suka tona asirin hukumar leken asiri ta kasar Amurka da aka san ta da sunan CIA, ta fannin yin amfani da fasahohin yanar gizo wajen kaddamar da juyin juya hali a kasashen duniya.

Misali, Amurka ta samarwa masu kin jinin gwamnati a kasashe kamar Tunisia da Masar, wani boyayyen tsarin sadarwa domin tabbatar da matasa ‘yan adawa masu son kawo tsaiko ga gwamnati, sun gujewa bincike da sa ido daga gwamnatocinsu yayin da suke gudanar da wannan aiki.

Ko da gwamnatin kasashen sun katse harkokin sadarwa a yunkurin hana ayyukan ‘yan adawar, hukumar CIA na iya samar da hidimomin sadarwa gare su, ta yadda za su iya ci gaba da ayyukansu. Alkaluman sun shaida cewa, a shekaru sama da goma, CIA ta riga ta kifar ko kuma ta yi yunkurin kifar da wasu halastattun gwamnatoci akalla 50, tare da hura wutar rikici a kasashe da dama.
Lallai, don tayar da tashin hankali a wasu kasashe har ma da hambarar da gwamnatin kasashen, Amurka ta yi ta rura wutar rikici a kasashen, ga shi kuma matakan da suka dauka da ma fasahohin zamani da suka yi amfani da su, gaskiya sun ba mu mamaki da ma damuwa.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Duk da haka, bayan da aka kaddamar da wadannan juyin juya halin, al’ummar kasashen sun tarar da cewa, abin da ya faru ba kamar yadda aka alkawarta musu ba, a maimakon yanayin kasashensu ya kara kyautata ba, kasashen sun tsunduma cikin mawuyacin hali na tashin hankali da tabarbarewar tattalin arziki da kuma wahalar rayuwa. Yanayin da ake ciki yanzu a Libya da Iraki da Ukraine dai duk sun shaida hakan.
Sai dai kamar Amurka ba ta jin kunyar munanan ayyukanta, har ma tana ganin hakan ya zama dole, duba da yadda mai taimakawa tsohon shugaban kasar Amurka kan harkokin tsaro, John R. Bolton ya yi na’am da rawar da Amurka ta taka wajen kaddamar da juyin mulki a wasu kasashe, a yayin da yake zantawa da manema labarai, har ya ce, juyin mulki a wasu kasashe “ya zama dole wajen tabbatar da moriyar kasar Amurka”.

To, kamar yadda Mr.Bolton ya fada, Amurka ba ta damu da yanayin da kasashen za su shiga bayan “juyin juya hali” ba, abin da kawai take tunani shi ne ko wadanda za su hau karagar mulkin kasashen za su yi mata biyayya, kuma hakan na faruwa ne sakamakon yadda kullum Amurka ke mai da moriyarta a gaban kome. Domin cimma moriyarta, Amurka tana daukar iya matakan da ta ga dama wajen tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe, har da hambarar da gwamnatocinsu.

Daidai da yadda Michael Lüders, marubucin kasar Jamus ya fada, kullum Amurka tana cewa tana daga cikin masu halin kirki, wadanda ke rungumar dimokuradiyya da ‘yanci a hakkin dan Adam, “amma a hakika abin ba haka yake ba, kawai suna bin moriyarsu ne.” (Lubabatu Lei)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kankan Da Kai Na Manzon Allah (SAW) I

Next Post

Yadda Hukumar CIA Ta Amurka Ke Aikata Mugunta Wajen Satar Bayanan Sirri

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

1 day ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

1 day ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

1 day ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

1 day ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

2 days ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

2 days ago
Next Post
Yadda Hukumar CIA Ta Amurka Ke Aikata Mugunta Wajen Satar Bayanan Sirri

Yadda Hukumar CIA Ta Amurka Ke Aikata Mugunta Wajen Satar Bayanan Sirri

LABARAI MASU NASABA

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.