ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ita Ce Sanadin Tashin Hankalin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Kasashen duniya sun dade da fuskantar “juyin juya hali” da ke da hannun kasar Amurka, wadanda aka kaddamar da sunan “‘Yanci” da “Dimokuradiyya” amma domin neman juyin mulkin kasashen, musamman a kasashen Afirka da gabas ta tsakiya da gabashin Turai da tsakiyar Asiya da sauransu, juyin juya hali da aka sawa sunayen “Rose Revolution” “Orange Revolution” “Tulip Revolution” “Jasmine Revolution” da sauransu.

Sai dai a cikin wadannan al’amura, fasahohin sadarwa na taka muhimmiyar rawa. Sanin kowa ne Kasar Amurka ce ke kan gaba a duniya ta fannin fasahohin zamani, musamman ma fasahar yanar gizo da ta yayata zuwa kasashen duniya a shekarun 1980, fasahohin da suka kuma samar mata tallafi wajen kaddamar da irin wannan juyin juya hali a kasashen da ta ga dama.

  • Mirginawar Rumbun Basuka A Jihohin Kano Da Kaduna

Cibiyar tunkarar harin kumfuta ta gaggawa ta kasar Sin da kamfanin kula da tsaron yanar gizo na 360 na kasar a kwanan nan sun fitar da wani rahoto bisa binciken da suka gudanar, inda suka tona asirin hukumar leken asiri ta kasar Amurka da aka san ta da sunan CIA, ta fannin yin amfani da fasahohin yanar gizo wajen kaddamar da juyin juya hali a kasashen duniya.

ADVERTISEMENT

Misali, Amurka ta samarwa masu kin jinin gwamnati a kasashe kamar Tunisia da Masar, wani boyayyen tsarin sadarwa domin tabbatar da matasa ‘yan adawa masu son kawo tsaiko ga gwamnati, sun gujewa bincike da sa ido daga gwamnatocinsu yayin da suke gudanar da wannan aiki.

Ko da gwamnatin kasashen sun katse harkokin sadarwa a yunkurin hana ayyukan ‘yan adawar, hukumar CIA na iya samar da hidimomin sadarwa gare su, ta yadda za su iya ci gaba da ayyukansu. Alkaluman sun shaida cewa, a shekaru sama da goma, CIA ta riga ta kifar ko kuma ta yi yunkurin kifar da wasu halastattun gwamnatoci akalla 50, tare da hura wutar rikici a kasashe da dama.
Lallai, don tayar da tashin hankali a wasu kasashe har ma da hambarar da gwamnatin kasashen, Amurka ta yi ta rura wutar rikici a kasashen, ga shi kuma matakan da suka dauka da ma fasahohin zamani da suka yi amfani da su, gaskiya sun ba mu mamaki da ma damuwa.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Duk da haka, bayan da aka kaddamar da wadannan juyin juya halin, al’ummar kasashen sun tarar da cewa, abin da ya faru ba kamar yadda aka alkawarta musu ba, a maimakon yanayin kasashensu ya kara kyautata ba, kasashen sun tsunduma cikin mawuyacin hali na tashin hankali da tabarbarewar tattalin arziki da kuma wahalar rayuwa. Yanayin da ake ciki yanzu a Libya da Iraki da Ukraine dai duk sun shaida hakan.
Sai dai kamar Amurka ba ta jin kunyar munanan ayyukanta, har ma tana ganin hakan ya zama dole, duba da yadda mai taimakawa tsohon shugaban kasar Amurka kan harkokin tsaro, John R. Bolton ya yi na’am da rawar da Amurka ta taka wajen kaddamar da juyin mulki a wasu kasashe, a yayin da yake zantawa da manema labarai, har ya ce, juyin mulki a wasu kasashe “ya zama dole wajen tabbatar da moriyar kasar Amurka”.

To, kamar yadda Mr.Bolton ya fada, Amurka ba ta damu da yanayin da kasashen za su shiga bayan “juyin juya hali” ba, abin da kawai take tunani shi ne ko wadanda za su hau karagar mulkin kasashen za su yi mata biyayya, kuma hakan na faruwa ne sakamakon yadda kullum Amurka ke mai da moriyarta a gaban kome. Domin cimma moriyarta, Amurka tana daukar iya matakan da ta ga dama wajen tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe, har da hambarar da gwamnatocinsu.

Daidai da yadda Michael Lüders, marubucin kasar Jamus ya fada, kullum Amurka tana cewa tana daga cikin masu halin kirki, wadanda ke rungumar dimokuradiyya da ‘yanci a hakkin dan Adam, “amma a hakika abin ba haka yake ba, kawai suna bin moriyarsu ne.” (Lubabatu Lei)

 

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Yadda Hukumar CIA Ta Amurka Ke Aikata Mugunta Wajen Satar Bayanan Sirri

Yadda Hukumar CIA Ta Amurka Ke Aikata Mugunta Wajen Satar Bayanan Sirri

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.