• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

byCMG Hausa
2 years ago
Amurka

Jiya Alhamis shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Henry Kissinger a birnin Beijing, hedkwatar kasar, inda ya kira Kissinger mai shekaru 100 da haihuwa tsohon aboki, tare da yaba wa gagarumar gudummowarsa a fannonin kara azama kan ci gaban hulda a tsakanin Sin da Amurka, da kyautata zumuncin da ke tsakanin al’ummomin kasashen 2. 

Yau shekaru 52 da suka wuce, Kissinger ya kasance mai ba da taimako ga shugaba Richard Nixon na Amurka na wancan lokaci ta fuskar tsaron kasa, da kuma manzon musamman, ya gana da tsoffin shugabannin kasar Sin, matakin da ya kaddamar da aikin maido da hulda tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

  • Xi Jinping Ya Ja Hankalin Kwararru A Fannonin Kimiyya Da Fasaha Da Su Mara Baya Da Yayata Ilimin Kimiyya

Ya zuwa yanzu, Kissinger ya ziyarci kasar Sin fiye da sau 100. Tsohon mai shekaru 100 da haihuwa, yana himmantuwa wajen kyautata tuntubar juna tsakanin Sin da Amurka.

Cikin ‘yan siyasar Amurka, Kissinger ya wakilci rukunin wadanda suke nacewa kan tattaunawa da kasar Sin, da kuma daidaita sabani yadda ya kamata. Wadannan ‘yan siyasan sun tsara manufofi masu dacewa game da kasar Sin bisa sanin ya kamata, a kokarin kiyaye muradun Amurka.

A duk lokacin da yake zantawa da shugaba Joe Biden na Amurka ta wayar tarho, ko kuma fuska da fuska, ko lokacin ganawarsa da mista Kissinger a jiya, shugaba Xi Jinping ya sha nanata cewa, dole ne a bi ka’idoji 3 wajen raya hulda a tsakanin Sin da Amurka ba tare da wata matsala ba, wato mutunta juna, da zaman tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa domin samun nasara tare. Su ne kuma darussan da aka koya daga yadda Sin da Amurka suka yi mu’amala da juna a baya, kana kuma, ka’idoji ne da kasashen 2 za su bi a sabon zamani, yayin da suke mu’amala da juna.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Yanzu haka kusoshin Amurka suna bukatar yin bitar abubuwan da suka faru a tarihi, kuma su kara sanin yadda suke kallon kasar Sin yadda ya kamata, da yadda za su yi mu’amala da kasar Sin, a kokarin biyan bukatunta. Idan sun san amsar hakan, fannonin hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Sin za su fadada, ba wai ta fuskar daidaita rikici kadai ba. Ko shakka babu, Amurka na bukatar hazakar Kissinger wajen raya hulda a tsakanin Sin da Amurka. (Tasallah Yuan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version