ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Jiya Alhamis shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Henry Kissinger a birnin Beijing, hedkwatar kasar, inda ya kira Kissinger mai shekaru 100 da haihuwa tsohon aboki, tare da yaba wa gagarumar gudummowarsa a fannonin kara azama kan ci gaban hulda a tsakanin Sin da Amurka, da kyautata zumuncin da ke tsakanin al’ummomin kasashen 2. 

Yau shekaru 52 da suka wuce, Kissinger ya kasance mai ba da taimako ga shugaba Richard Nixon na Amurka na wancan lokaci ta fuskar tsaron kasa, da kuma manzon musamman, ya gana da tsoffin shugabannin kasar Sin, matakin da ya kaddamar da aikin maido da hulda tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

  • Xi Jinping Ya Ja Hankalin Kwararru A Fannonin Kimiyya Da Fasaha Da Su Mara Baya Da Yayata Ilimin Kimiyya

Ya zuwa yanzu, Kissinger ya ziyarci kasar Sin fiye da sau 100. Tsohon mai shekaru 100 da haihuwa, yana himmantuwa wajen kyautata tuntubar juna tsakanin Sin da Amurka.

ADVERTISEMENT

Cikin ‘yan siyasar Amurka, Kissinger ya wakilci rukunin wadanda suke nacewa kan tattaunawa da kasar Sin, da kuma daidaita sabani yadda ya kamata. Wadannan ‘yan siyasan sun tsara manufofi masu dacewa game da kasar Sin bisa sanin ya kamata, a kokarin kiyaye muradun Amurka.

A duk lokacin da yake zantawa da shugaba Joe Biden na Amurka ta wayar tarho, ko kuma fuska da fuska, ko lokacin ganawarsa da mista Kissinger a jiya, shugaba Xi Jinping ya sha nanata cewa, dole ne a bi ka’idoji 3 wajen raya hulda a tsakanin Sin da Amurka ba tare da wata matsala ba, wato mutunta juna, da zaman tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa domin samun nasara tare. Su ne kuma darussan da aka koya daga yadda Sin da Amurka suka yi mu’amala da juna a baya, kana kuma, ka’idoji ne da kasashen 2 za su bi a sabon zamani, yayin da suke mu’amala da juna.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Yanzu haka kusoshin Amurka suna bukatar yin bitar abubuwan da suka faru a tarihi, kuma su kara sanin yadda suke kallon kasar Sin yadda ya kamata, da yadda za su yi mu’amala da kasar Sin, a kokarin biyan bukatunta. Idan sun san amsar hakan, fannonin hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Sin za su fadada, ba wai ta fuskar daidaita rikici kadai ba. Ko shakka babu, Amurka na bukatar hazakar Kissinger wajen raya hulda a tsakanin Sin da Amurka. (Tasallah Yuan)

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.