ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Jiya Alhamis shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Henry Kissinger a birnin Beijing, hedkwatar kasar, inda ya kira Kissinger mai shekaru 100 da haihuwa tsohon aboki, tare da yaba wa gagarumar gudummowarsa a fannonin kara azama kan ci gaban hulda a tsakanin Sin da Amurka, da kyautata zumuncin da ke tsakanin al’ummomin kasashen 2. 

Yau shekaru 52 da suka wuce, Kissinger ya kasance mai ba da taimako ga shugaba Richard Nixon na Amurka na wancan lokaci ta fuskar tsaron kasa, da kuma manzon musamman, ya gana da tsoffin shugabannin kasar Sin, matakin da ya kaddamar da aikin maido da hulda tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

  • Xi Jinping Ya Ja Hankalin Kwararru A Fannonin Kimiyya Da Fasaha Da Su Mara Baya Da Yayata Ilimin Kimiyya

Ya zuwa yanzu, Kissinger ya ziyarci kasar Sin fiye da sau 100. Tsohon mai shekaru 100 da haihuwa, yana himmantuwa wajen kyautata tuntubar juna tsakanin Sin da Amurka.

ADVERTISEMENT

Cikin ‘yan siyasar Amurka, Kissinger ya wakilci rukunin wadanda suke nacewa kan tattaunawa da kasar Sin, da kuma daidaita sabani yadda ya kamata. Wadannan ‘yan siyasan sun tsara manufofi masu dacewa game da kasar Sin bisa sanin ya kamata, a kokarin kiyaye muradun Amurka.

A duk lokacin da yake zantawa da shugaba Joe Biden na Amurka ta wayar tarho, ko kuma fuska da fuska, ko lokacin ganawarsa da mista Kissinger a jiya, shugaba Xi Jinping ya sha nanata cewa, dole ne a bi ka’idoji 3 wajen raya hulda a tsakanin Sin da Amurka ba tare da wata matsala ba, wato mutunta juna, da zaman tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa domin samun nasara tare. Su ne kuma darussan da aka koya daga yadda Sin da Amurka suka yi mu’amala da juna a baya, kana kuma, ka’idoji ne da kasashen 2 za su bi a sabon zamani, yayin da suke mu’amala da juna.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Yanzu haka kusoshin Amurka suna bukatar yin bitar abubuwan da suka faru a tarihi, kuma su kara sanin yadda suke kallon kasar Sin yadda ya kamata, da yadda za su yi mu’amala da kasar Sin, a kokarin biyan bukatunta. Idan sun san amsar hakan, fannonin hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Sin za su fadada, ba wai ta fuskar daidaita rikici kadai ba. Ko shakka babu, Amurka na bukatar hazakar Kissinger wajen raya hulda a tsakanin Sin da Amurka. (Tasallah Yuan)

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Next Post
Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Amurka

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Amurka

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.