• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Dauke Da Nauyin Dakatar Da Kisan Fararen Hula A Rafah

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da dubban Falasdinawa dake arewacin zirin Gaza ke tserewa zuwa kudanci, sakamakon yakin da sojojin Isra’ila suka kaddamar na murkushe kungiyar Hamas tun daga ranar 7 ga watan Oktoban bara, masharhanta da dama na ganin lokaci na kara kurewa, na kawo karshen wannan tashin hankali, duba da cewa ga alama matakan sojin da Isra’ilan ke dauka ba abu ne da zai kare a nan kusa ba.

Ya zuwa yanzu, hare-haren sojojin Isra’ila sun kora sama da mutune miliyan guda wani lungu dake kudancin Gaza, inda birnin Rafah ya zamo “Gaba kura baya sayaki” ga masu tserewa hare-haren Isra’ila.

  • Xi Jinping Ya Nanata Wajibcin Yin Kwaskwarima Da Kirkire-Kirkire Cikin Hakikanin Hali A Lardin Hunan
  • Majasirdin Sarkin Zazzau, Alhaji Yusuf Saleh Barde Ya Rasu

Duk da jan hankali da aka sha yi masa, firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya dage cewa sai sojojinsa sun kaddamar da hare-hare a Rafah. Alkaluma sun nuna cewa, kafin wannan tashin hankali, Rafah na da kimanin mutane 275,000 ne kacal, amma yanzu mutane sama da miliyan 1.4 ke cunkushe a cikinsa, a yanayi na matukar bukatar jin kai.

Majalissar Dinkin Duniya, da kungiyar tarayyar Turai ta EU, sun nuna damuwa game da mummunan tasirin da hare-hare a Rafah za su yi ga fararen hula. A daya hannun kuma, a baya bayan nan ita ma kasar Sin ta bayyana damuwa, game da yadda rikicin Falasdinu da Isra’ila ya haura watanni 5, kana yanayin jin kai a wurin ke kara tabarbarewa, don haka ta bayyana wajibcin gaggauta tsagaita wuta nan take, da yin iyakacin kokarin kiyaye rayukan fararen hula, da kuma rage matsalolin jin kai.

Mun san dai da fari, Amurka na sahun gaba wajen marawa Isra’ila baya a wannan yaki mai muni, amma a yanzu ta fara sauya matsaya, har ma an jiyo shugaba Joe Biden na Amurkan na cewa, kaiwa birnin Rafah hare-hare zai zama kuskure mai matukar muni.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

La’akari da goyon baya da Amurkan ta nunawa Isra’ila tsawon lokaci kan wannan batu, ta hanyar maimaita dakatar da kudurin kwamitin tsaron MDD game da tsagaita wuta a Gaza, da tarin makamai da ta rika aikewa Isra’ila, da ma yadda kalaman sauya matsayar ta suka fara sanya Isra’ilan nuna alamun sassautawa. Muna iya cewa idan akwai wani karfi da zai iya sauya yanayin da ake ciki a Gaza ba zai wuce Amurka ba. Ko da yake wasu masu sharhi sun ce gwamnatin Amurka mai ci ta fara sauya matsaya ne saboda al’ummunta sun fara bore, inda a baya bayan nan masu zanga-zanga a jihar Michigan, suka rika daga kyallaye masu dauke da sakon “Idan ba a dakatar da wuta ba, ba za a yi zabe ba”.

Koma dai mene ne ke faruwa a siyasar cikin gidan Amurka? Abun da ya fi damun al’ummun duniya masu son zaman lafiya, shi ne fatan ganin Amurka ta yi abun da ya dace, ta saurari ra’ayoyin sauran sassa, ta kuma goyi bayan dakatar da bude wuta a Gaza, da wanzar da zaman lafiya mai dorewa a yankin gabas ta tsakiya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Direba Da Fasinjoji 18 A Katsina

Next Post

CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 2

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

9 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

10 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

11 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

12 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

13 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

15 hours ago
Next Post
CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1

CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 2

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.