• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Fara Dandana Kudar Manufar Kakaba Harajin Kwastam

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Amurka

Asusun ajiyar kudade na kasar Amurka ya fitar da takardar bayani dangane da yanayin tattalin arzikin da kasar take ciki a jiya Laraba, inda aka nuna cewa, ganin yadda ake kara samun rashin tabbas a fannin tattalin arziki, makomar sassa da dama a kasar ta kara tabarbarewa. Tuni dai a ranar Talata, asasun ba da lamuni na duniya wato IMF ya fitar da rahoton hangen nesa kan tattalin arzikin duniya, inda ya rage hasashen da aka yi wa karuwar tattalin arzikin Amurka ta shekara ta 2025, raguwar da ta kai kaso 0.9 bisa dari, idan aka kwatanta da hasashen da aka yi a watan Janairun bana, al’amarin da ya sa Amurka ta zama kasa da aka fi rage hasashen karuwar tattalin arzikinta daga cikin kasashe masu ci gaba.

 

Kwanan nan ne Amurkawa daga duk fadin kasar suka fito kan tituna domin nuna adawa ga manufar gwamnatin kasar ta kakaba karin harajin kwastam. Baya ga jihar California, a ranar Laraba, akwai sauran wasu jihohi 12 da suka daukaka kara kan gwamnatin tarayya, inda suka bukaci a dakatar da irin wannan manufa, wadda a cewarsu, take kawo rudani sosai ga tattalin arzikin Amurka. Lamarin ya kuma bayyana dalilin da ya sa yawan mutanen da suka goyi bayan shugaban Amurka ta fannin tattalin arziki ya yi matukar raguwa daga farkon sabon wa’adin mulkinsa zuwa yanzu. Kwararan shaidu sun nuna cewa, kara sanya harajin kwastam bai haifar da karuwar samun kudi ga kasar ba, akasin haka ma aka samu, inda lamarin ya janyo tafiyar hawainiya ga tattalin arziki da kara tsawwala farashin kaya, gami da raguwar hasashen tattalin arziki da aka yi.

 

Ya kamata Amurka ta fahimci matsalolin da take fuskanta, da koyon darussa daga ciki, don warware matsalar cinikayya ta hanyar gudanar da shawarwari cikin adalci tare da abokan cinikayyarta. Idan Amurka ta ci gaba da kawo barazana ko yaudarar sauran kasashe, za ta kara dandana kudarta, kuma ba za ta kara samun nasara ba ko kadan. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Next Post
Yayin Da Ake Fuskantar Daminar Bana: Sabbin Hare-hare Na Barazana Ga Shirin Wadata Kasa Da Abinci

Yayin Da Ake Fuskantar Daminar Bana: Sabbin Hare-hare Na Barazana Ga Shirin Wadata Kasa Da Abinci

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.