• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

by Abubakar Abba
2 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoma a Nijeriya sun nuna matuƙar damuwarsu kan yadda shinkafa da masarar da ake shigowa da su daga ƙasashen waje suka mamaye kasuwannin ƙasar nan, wanda kuma ake sayar da su kusan a farashi guda da kayan abincin da ake noma a cikin gida. 

Manoman wadanda suka nuna takaicinsu a shafin Tiwita, sun ce tsare-tsaren Shugaban ƙasa Bola Tinubu na kashe darajar noman shinkafa da masara a cikin gida. 

Wannan koken nasu dai na zuwa ne a daidai lokacin da farashin kayayyakin abinci ke ci gaba da sauƙa a sassa daban-daban na ƙasar nan. 

  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Duk da yake jama’a suna nuna jin daɗinsu kan yadda farashin kayan masarufi ke sauƙa, su kuma manoma na nuna hakan a matsayin abun damuwa. Sun ce, kayan abincin na sauƙa ne sakamakon shigo da su da ake yi daga ƙasashen waje. 

Idan za a tuna dai a watan Yuli na shekarar da ta gabata gwamantin tarayya ta sanar da janye takunkumi na tsawon kwanaki 150 ga shigo da shinkafa da masara da sauran kayan abinci da nufin kawo sauƙi wa al’ummar ƙasar nan. 

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

A zagayen duba farashin kayayyakin da aka gudanar a kasuwannin ƙasar nan, ya nuna cewa, farashin 50-kilogramme na buhun shinkafa ƴar gida ana sayar da shi ne a kan naira dubu 65,000 zuwa naira 68,000, inda kuma ake sayar da masara kan naira dubu 35,000 zuwa 37,000 a kan kowani buhu, yayin da na ƙasashen waje ke kaiwa naira 83,000 kan buhu guda. 

Wannan gagarumin ragin da aka samu ya sanya manoman cikin gida na nuna hakan a matsayin ƙalubale ga ci gaba da noman a Nijeriya.

Sai dai kuma babban matsalar da ake fuskanta a harkar noma a Nijeriya shi ne tsadar takin zamani da sauran kayan aikin gona a Nijeriya, lamarin da ke sanya abun da manoman cikin gida ke fitarwa na tsada, amma kuma in sun kai kasuwa farashin nasu sai ya yi gogayya da na ƙasashen waje lamarin da ke sanya jama’a zaɓar na ƙasashen waje musamman saboda rashin gyara yayin dafawa. 

da yake magana kan wannan lamarin, Farfesa Godwin Oyedokun na jam’iyar Lead City da ke Ibadan, ya ce rubibin sayen shinkafa da masarar ƙasashen waje fiye da na cikin gida a kasuwanni na matuƙar shafan manoman cikin gida kuma hakan na sanyaya gwiwar ƙoƙarinsu na gogayyar wadata ƙasa da abinci. 

Ya ce a maimakon a bar manoma su ci gaba da kokawa wanda hakan ba ci gaba ne ga ƙasar nan, akwai buƙatar gwamnatin tarayya ta nemi manoman su zauna tare da jin damuwowinsu gami da daukan matakan shawo musu kansu domin amfanun kowa a ƙasar nan. 

“Ina bai wa gwamnati shawara ta samar da tsare-tsaren da za su taimaki amfanin gonan cikin gida da ake samarwa, kamar samar da tallafi, samar rance, zuba hannun jari a ɓangaren noma da fasahohin zamanin da za su taimaka wa manoma, hakan zai sanya suke fitar da amfani gona cikin sauƙi.”

Babban shehin malamin bokon ya kuma ce bai wa manoma damarmakin shiga kasuwannin yadda ya kamata zai taimaka musu wajen samun farashi na adalci, ya kuma nemi a horas da manoma kan dabarun noma na zamani da amfani da fasahohi domin ƙara sauƙaƙa harkokin noma a ƙasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MaizeMasaraNomaRiceShinkafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Next Post

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

1 day ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.