• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

by Abubakar Abba
43 seconds ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoma a Nijeriya sun nuna matuƙar damuwarsu kan yadda shinkafa da masarar da ake shigowa da su daga ƙasashen waje suka mamaye kasuwannin ƙasar nan, wanda kuma ake sayar da su kusan a farashi guda da kayan abincin da ake noma a cikin gida. 

Manoman wadanda suka nuna takaicinsu a shafin Tiwita, sun ce tsare-tsaren Shugaban ƙasa Bola Tinubu na kashe darajar noman shinkafa da masara a cikin gida. 

Wannan koken nasu dai na zuwa ne a daidai lokacin da farashin kayayyakin abinci ke ci gaba da sauƙa a sassa daban-daban na ƙasar nan. 

  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Duk da yake jama’a suna nuna jin daɗinsu kan yadda farashin kayan masarufi ke sauƙa, su kuma manoma na nuna hakan a matsayin abun damuwa. Sun ce, kayan abincin na sauƙa ne sakamakon shigo da su da ake yi daga ƙasashen waje. 

Idan za a tuna dai a watan Yuli na shekarar da ta gabata gwamantin tarayya ta sanar da janye takunkumi na tsawon kwanaki 150 ga shigo da shinkafa da masara da sauran kayan abinci da nufin kawo sauƙi wa al’ummar ƙasar nan. 

Labarai Masu Nasaba

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

A zagayen duba farashin kayayyakin da aka gudanar a kasuwannin ƙasar nan, ya nuna cewa, farashin 50-kilogramme na buhun shinkafa ƴar gida ana sayar da shi ne a kan naira dubu 65,000 zuwa naira 68,000, inda kuma ake sayar da masara kan naira dubu 35,000 zuwa 37,000 a kan kowani buhu, yayin da na ƙasashen waje ke kaiwa naira 83,000 kan buhu guda. 

Wannan gagarumin ragin da aka samu ya sanya manoman cikin gida na nuna hakan a matsayin ƙalubale ga ci gaba da noman a Nijeriya.

Sai dai kuma babban matsalar da ake fuskanta a harkar noma a Nijeriya shi ne tsadar takin zamani da sauran kayan aikin gona a Nijeriya, lamarin da ke sanya abun da manoman cikin gida ke fitarwa na tsada, amma kuma in sun kai kasuwa farashin nasu sai ya yi gogayya da na ƙasashen waje lamarin da ke sanya jama’a zaɓar na ƙasashen waje musamman saboda rashin gyara yayin dafawa. 

da yake magana kan wannan lamarin, Farfesa Godwin Oyedokun na jam’iyar Lead City da ke Ibadan, ya ce rubibin sayen shinkafa da masarar ƙasashen waje fiye da na cikin gida a kasuwanni na matuƙar shafan manoman cikin gida kuma hakan na sanyaya gwiwar ƙoƙarinsu na gogayyar wadata ƙasa da abinci. 

Ya ce a maimakon a bar manoma su ci gaba da kokawa wanda hakan ba ci gaba ne ga ƙasar nan, akwai buƙatar gwamnatin tarayya ta nemi manoman su zauna tare da jin damuwowinsu gami da daukan matakan shawo musu kansu domin amfanun kowa a ƙasar nan. 

“Ina bai wa gwamnati shawara ta samar da tsare-tsaren da za su taimaki amfanin gonan cikin gida da ake samarwa, kamar samar da tallafi, samar rance, zuba hannun jari a ɓangaren noma da fasahohin zamanin da za su taimaka wa manoma, hakan zai sanya suke fitar da amfani gona cikin sauƙi.”

Babban shehin malamin bokon ya kuma ce bai wa manoma damarmakin shiga kasuwannin yadda ya kamata zai taimaka musu wajen samun farashi na adalci, ya kuma nemi a horas da manoma kan dabarun noma na zamani da amfani da fasahohi domin ƙara sauƙaƙa harkokin noma a ƙasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MaizeMasaraNomaRiceShinkafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Related

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 day ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 week ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

2 weeks ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

3 weeks ago

LABARAI MASU NASABA

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.