• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Za Ta Aika Wa Ukraine Karin Makamai Masu Linzami

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Amurka Za Ta Aika Wa Ukraine Karin Makamai Masu Linzami
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu jami’an Amurka biyu sun ce shugaba Joe Biden ne ya amince da matakin tura makaman.
Amurka za ta aika wa Ukraine makami mai linzami na Patriot, a cewar wasu jami’an Amurka biyu, a matsayin maida martani ga kiraye-kirayen da Kyib ta yi na neman taimakon gaggawa wajen samun karin na’urorin kariya ta sama yayin da kasar ke fama da hare-haren Rasha a yankin Kharkib.
Wannan zai zama makami mai linzami samfurin Patriot na biyu da Amurka ta bai wa Ukraine, ko da yake ma’aikatar tsaron Pentagon ta tura makamai masu linzami da ba a bayyana adadinsu ba.

  • Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai
  • Sin: Amurka Ta Sake Yada Karairayi Ta Hanyar Zargin Sin Da Tallafawa Rasha Da Makamai

Sauran kasashen kawancen Ukraine da suka hada da Jamus, su ma sun sama wa Ukraine da na’urorin kariya ta sama da kuma alburusai.

Jami’an na Amurka biyu sun yi magana ne bisa sharadin a sakaya sunayensu saboda ba a sanar da matakin ba. Jaridar New York Times ce ta fara ba da rahoton matakin.
A karshen watan da ya gabata, shugaban Ukraine Bolodymyr Zelenskyy ya nemi karin makami mai linzamin Patriot na Amurka, yana mai cewa makaman za su taimaka wa dakarunsa wajen kakkabo bama-bamai kusan 3,000 da Ra-sha ke harbawa cikin kasar duk wata.

Da yake magana a Madrid, Zelenskyy ya ce har yanzu Ukraine na bukatar karin wasu makaman guda bakwai don dakile hare-haren da Rasha ke kai wa kan manyan na’urorin samar da wutar lantarki da yankunan farar hula, da ku-ma wuraren soja.

Ya ce Ukraine na bukatar biyu daga cikin makaman don kare Kharkib, inda Rasha ta kaddamar da hare-haren tsallaken iyaka a ranar 10 ga watan Mayu, lamarin da ya sa har yanzu sojojin Ukraine ke gwagwarmaya.

Labarai Masu Nasaba

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

“Idan muna da wadannan makaman na Patriot na zamani, jiragen sama na Ra-sha ba za su iya zuwa kusa su jefa bama-bamai a kan farar hula da sojoji ba,” in ji Zelenskyy a wani taron manema labarai a babban birnin Sipaniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Next Post

Rundunar Sojin Ƙasan Nijeriya,Ta Yi Bikin Yaye Sabbin Sojoji 5,937

Related

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

7 days ago
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu
Kasashen Ketare

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

1 week ago
Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine
Kasashen Ketare

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

2 weeks ago
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari
Kasashen Ketare

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

2 weeks ago
Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

2 weeks ago
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka
Kasashen Ketare

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

2 weeks ago
Next Post
Rundunar Sojin Ƙasan Nijeriya,Ta Yi Bikin Yaye Sabbin Sojoji 5,937

Rundunar Sojin Ƙasan Nijeriya,Ta Yi Bikin Yaye Sabbin Sojoji 5,937

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.