• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bankado Badakalar Da Ake Zargin Shugaban Hukumar NIRSAL Ya Yi Kan Noman Alkama

by Sabo Ahmad
3 years ago
in Labarai
0
An Bankado Badakalar Da Ake Zargin Shugaban Hukumar NIRSAL Ya Yi Kan Noman Alkama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An dakatar da Babban manajan darakta na hukumar bayar da tallafi ga wadanda suka yi asarar amfanin gona kamar yadda jaridar Daily Tust Saturday ta ruwaito.

Bayanai sun tabbatar da cewa, an tunbuke Aliyu Abdulhameed ne saboda yawan zarge-zargen da ake yi a kansa na cin-hanci da karbar rashawa wadanda suka hada da badakalar zunzurutun kudin da suka kai naira biliyan 5.6, a shekara ta 2018, kan noman alkama a jihar Kano da Jigawa, wadanda ake zargin jami’a hukumar ta NIRSAL da jefa wa a cikin lalitarsu.

  • Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

Yadda rahoton jaridar Daily Trust ya tona asirin wata badakala a hukumar NIRSAL
A wani rahoton bincike da wannan jaridar ta wallafa a cikin watan Janairun bana wanda ta yi bincike a kan yadda bashin da aka ci na biliyoyin nairar da hukumar NIRSAL ta tsaya aka ci ga wasu kamfanoni guda uku domin yin noman rani a wata gona mai fadin hrkta 20,000 a jihar Kano da Jigawa wanda aka hada baki da jami’an hukumar ta NIRSAL.

Lokacin gudanar da bincike, jaridar DAILY TRUST ta ranar Lahadi,ta je garin da wannan abin ya faru, da ke jihohin arewa maso yamma, domin ji daga majiya mai tushe.
Shugabannin wannan al’umma, sun bayyana cewa, an gaya musu, an kikiro wannan shirin ne domin Tallafa wa kananan manoman da yawansu ya kai 20,000. Wasu daga cikin manoman sun ce, ba za su taba yafe wa ba, da yaudarar da aka yi musu. Bayan na bayar da gonata domin gudanar da wannan shiri, sun yi alkawarin za su ba ni taki, za kuma su haka min rijiya ko su taimaka min yadda zan jawo ruwa, amma ashe duk yaudara ta suke yi, ba su yi min komai ba.

Araya Alhaji Idi, wani shi ma daga cikin manoman, daya daga cikin manoman a garin Ringim da ke jihar Jigawa, ya bayyana cewa, tun da suka muka yi maga da su da farko ba su sake dawo wa ba, kuma ko ta waya ba su kira mu ba, domin sanar da al’umma halin da ake ciki ba, sun bar mu a igiyar ruwa. In ji shi.
Sai dai shugaban hukumar ta NIRSAL, ya musanta wannan zargin da ake yi masa, wanda ya ce, wannan turka-turkar da ta taso, wasu mutane ne daga gefe, kuma suke kokarin rura wutar riki domin su bata masa suna da kuma hukumar.

Labarai Masu Nasaba

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

Sai dai idan muka lura da rahoton da jaridar DAILY TRUST ta bayar, ya sa, hukumar EFCC ta nemi Manajan daraktan tare da wasu ma’akatan na NIRSAL domin su yi bayani kan zargin da ake yi musu na mallake makudan kudi da sunan yin aiki, kuma ba a yi aikin ba.
Bayan binciken hukumar EFCC, ita ma hukumar ICPC da jami’an ‘yansanda su ma suna bincike a kan zargin da ake yi na badakalar wasu ayyuka.

An nemi shugaban ya je ya yi bayani, ranar Alhamis din da ta gabata jim kadan bayan kan wannan zargin da ake yi masa, sai dai har zuwa lokaci kammala wannan rahoto, bai mika matsayin nasa ga wani wanda zai ci gaba da tafiyar da aikin nasa ba, kafin a san cikakken halin da ake ciki.

An nemi jin da bakin shugaban ko kuma jami’in hulda da jama’a na hukumar, amma duka abin ya ci tura.

Wata majiyar labarai, mai tushe, ta nuna cewa, ba a kori Abdulhameed ba, sai dai ya dakata ne domin bayar da damar gudanar da cikakken bincike kan zargin da ake yi masa, wanda hukumar EFCC da ta ICPC da kuma jami’an tsaro na farin kaya ke yi masa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

Next Post

‘Yansanda Sun Gano Wurin Da IPOB Ke Hada Bama-Bamai

Related

Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

57 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

13 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

15 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

16 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

17 hours ago
Next Post
Miji Ya Hallaka Matarsa A Kan Ruwan Sha A Legas

'Yansanda Sun Gano Wurin Da IPOB Ke Hada Bama-Bamai

LABARAI MASU NASABA

Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.