ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bankado Badakalar Da Ake Zargin Shugaban Hukumar NIRSAL Ya Yi Kan Noman Alkama

by Sabo Ahmad
4 years ago
Nirsal

An dakatar da Babban manajan darakta na hukumar bayar da tallafi ga wadanda suka yi asarar amfanin gona kamar yadda jaridar Daily Tust Saturday ta ruwaito.

Bayanai sun tabbatar da cewa, an tunbuke Aliyu Abdulhameed ne saboda yawan zarge-zargen da ake yi a kansa na cin-hanci da karbar rashawa wadanda suka hada da badakalar zunzurutun kudin da suka kai naira biliyan 5.6, a shekara ta 2018, kan noman alkama a jihar Kano da Jigawa, wadanda ake zargin jami’a hukumar ta NIRSAL da jefa wa a cikin lalitarsu.

  • Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

Yadda rahoton jaridar Daily Trust ya tona asirin wata badakala a hukumar NIRSAL
A wani rahoton bincike da wannan jaridar ta wallafa a cikin watan Janairun bana wanda ta yi bincike a kan yadda bashin da aka ci na biliyoyin nairar da hukumar NIRSAL ta tsaya aka ci ga wasu kamfanoni guda uku domin yin noman rani a wata gona mai fadin hrkta 20,000 a jihar Kano da Jigawa wanda aka hada baki da jami’an hukumar ta NIRSAL.

ADVERTISEMENT

Lokacin gudanar da bincike, jaridar DAILY TRUST ta ranar Lahadi,ta je garin da wannan abin ya faru, da ke jihohin arewa maso yamma, domin ji daga majiya mai tushe.
Shugabannin wannan al’umma, sun bayyana cewa, an gaya musu, an kikiro wannan shirin ne domin Tallafa wa kananan manoman da yawansu ya kai 20,000. Wasu daga cikin manoman sun ce, ba za su taba yafe wa ba, da yaudarar da aka yi musu. Bayan na bayar da gonata domin gudanar da wannan shiri, sun yi alkawarin za su ba ni taki, za kuma su haka min rijiya ko su taimaka min yadda zan jawo ruwa, amma ashe duk yaudara ta suke yi, ba su yi min komai ba.

Araya Alhaji Idi, wani shi ma daga cikin manoman, daya daga cikin manoman a garin Ringim da ke jihar Jigawa, ya bayyana cewa, tun da suka muka yi maga da su da farko ba su sake dawo wa ba, kuma ko ta waya ba su kira mu ba, domin sanar da al’umma halin da ake ciki ba, sun bar mu a igiyar ruwa. In ji shi.
Sai dai shugaban hukumar ta NIRSAL, ya musanta wannan zargin da ake yi masa, wanda ya ce, wannan turka-turkar da ta taso, wasu mutane ne daga gefe, kuma suke kokarin rura wutar riki domin su bata masa suna da kuma hukumar.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sai dai idan muka lura da rahoton da jaridar DAILY TRUST ta bayar, ya sa, hukumar EFCC ta nemi Manajan daraktan tare da wasu ma’akatan na NIRSAL domin su yi bayani kan zargin da ake yi musu na mallake makudan kudi da sunan yin aiki, kuma ba a yi aikin ba.
Bayan binciken hukumar EFCC, ita ma hukumar ICPC da jami’an ‘yansanda su ma suna bincike a kan zargin da ake yi na badakalar wasu ayyuka.

An nemi shugaban ya je ya yi bayani, ranar Alhamis din da ta gabata jim kadan bayan kan wannan zargin da ake yi masa, sai dai har zuwa lokaci kammala wannan rahoto, bai mika matsayin nasa ga wani wanda zai ci gaba da tafiyar da aikin nasa ba, kafin a san cikakken halin da ake ciki.

An nemi jin da bakin shugaban ko kuma jami’in hulda da jama’a na hukumar, amma duka abin ya ci tura.

Wata majiyar labarai, mai tushe, ta nuna cewa, ba a kori Abdulhameed ba, sai dai ya dakata ne domin bayar da damar gudanar da cikakken bincike kan zargin da ake yi masa, wanda hukumar EFCC da ta ICPC da kuma jami’an tsaro na farin kaya ke yi masa.

Nirsal
Sabo Ahmad
+ postsBio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Miji Ya Hallaka Matarsa A Kan Ruwan Sha A Legas

'Yansanda Sun Gano Wurin Da IPOB Ke Hada Bama-Bamai

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.