• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bude Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Bude Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bude babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin JKS karo na 20, da misalin karfe 10 na safiyar yau Lahadi a Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Wakilan jam’iyyar, gami da wadanda aka ba su goron gayyata na musamman sama da 2300 sun halarci taron, tare da wasu da ba ’yan jam’iyyar kwaminis din ba da sauransu. Za kuma a rufe taron a ranar 22 ga wata.

  • Gobe Ne Za A Gudanar Da Babban Taron Wakilan JKS Na 20

A wajen taron, za’a saurara, gami da duba rahoton aiki na kwamitin kolin JKS na 19, da duba rahoton aikin da kwamitin ladabtarwa na kwamitin koli na JKS na 19 ya gabatar. Kana, za’a amince da gyararren shiri na kundin ka’idojin jam’iyyar JKS, da kuma zabar membobin kwamitin kolin jam’iyyar da na kwamitin ladabtarwar jam’iyyar a sabon zagaye.

Jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin mai tarihin shekaru 101, ta shafe tsawon shekaru 73 tana kan karagar mulkin kasar Sin, wato tun kafuwar Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin.

Babban taron wakilan jam’iyyar, gami da kwamitin kolinta, su ne hukumar koli ta jam’iyyar. A kan gudanar da babban taron wakilan jam’iyyar a duk bayan shekaru biyar.
A wajen taron, shugaba Xi Jinping ya gabatar da muhimmin rahoto, a madadin kwamitin kolin jam’iyyar na 19.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Xi ya ce, a shekaru 10 da suka gabata, yawan GDPn kasar Sin ya karu daga kudin Sin Yuan tiriliyan 54, har zuwa tiriliyan 114, kana jimillar tattalin arzikin kasar Sin ta dauki kaso 18.5 bisa dari, na jimillar tattalin arzikin duk duniya, adadin da ya karu da kaso 7.2 bisa dari, wanda ya sa kasar ta zama ta biyu a duniya.

Shugaba Xi ya kuma ce, kasar Sin ta zama babbar aminiyar cinikayya ga kasashe da yankuna sama da 140, kuma jimillar kudin cinikayyar kayayyaki ta kasar tana kan gaba a duniya, kana, yawan jarin waje da kasar Sin ta jawo, da yawan jarin da ta zuba a sauran kasashe duk suna kan gaba.

A halin yanzu kasar Sin tana habaka bude kofarta ga kasashen waje a fannoni daban-daban.

Xi ya kara da cewa, kasar Sin ta samu babban ci gaba wajen raya wasu muhimman fasahohi, da kara bunkasa sabbin sana’o’i da dama, ciki har da zirga-zirgar kumbuna masu dauke da dan Adam a sararin samaniya, da binciken duniyar wata da duniyar Mars, da binciken yankin ruwan teku mai zurfi, da nazarin manyan na’urori masu kwakwalwa, da taurarin dan Adam, da amfani da makamashin nukiliya don samar da wutar lantarki, da kera manyan jiragen sama, da harhada magunguna da sauransu, al’amarin da ya sa Sin ta shiga jerin kasashen dake kan gaba a duniya, wajen yin kirkire-kirkire.

Har wa yau, shugaba Xi ya nuna cewa, ya dace kasar Sin ta raya ingantaccen tsarin tattalin arziki irin na kasuwa mai salon gurguzu, da tsayawa gami da kyautata babban tsarin tattalin arziki irin na gurguzu, da kara habaka tattalin arziki irin na gwamnati, da kuma karfafa gwiwa da jagorantar ayyukan raya tattalin arzikin da ba na gwamnati ba, ta yadda kasuwannin kasar za su kara taka muhimmiyar rawa wajen daidaita albarkatu, kuma gwamnatin kasar ita ma za ta kara taka rawarta.

Xi ya jaddada cewa, ya dace a raya tsarin sana’o’i irin na zamani, da maida hankali sosai kan raya sassan da suka shafi hada-hadar kudade kai-tsaye, da raya sabbin masana’antu, da gaggauta gina kasar Sin mai karfin yin kere-kere, mai karfin binciken sararin samaniya, mai karfin zirga-zirgar ababen hawa, mai karfin amfani da yanar gizo ta intanet, mai karfin fasahar sadarwar zamani da sauransu.

Har wa yau, ya kamata a nuna azama wajen farfado da yankunan karkara daga dukkan fannoni, da nuna fifiko wajen samar da ci gaban ayyukan noma da yankunan karkara, da kara saurin raya kasar Sin mai karfin aikin noma.

Shugaba Xi ya kara da cewa, ana bukatar a ci gaba da habaka bude kofar kasar Sin ga kasashen ketare, da gagguta raya kasar mai karfin harkokin kasuwanci, da taimakawa ci gaban aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, a wani kokari na kiyaye tsarin tattalin arzikin duniya, da huldar tattalin arziki, da kasuwanci dake kunshe da bangarori daban-daban. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Sa Hannun Gwamnatin Zamfara ‘Yan Daba Suka Farmake Mu – Dan Takarar Gwamna A PDP

Next Post

Xi Ya Yi Bayani Kan Muhimman Nasarori 3 Da Aka Cimma Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

3 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

5 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

21 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
Xi Ya Yi Bayani Kan Muhimman Nasarori 3 Da Aka Cimma Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Xi Ya Yi Bayani Kan Muhimman Nasarori 3 Da Aka Cimma Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
JKS

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.