ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Bayani Kan Muhimman Nasarori 3 Da Aka Cimma Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

by CMG Hausa
4 years ago
Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a yau Lahadi cewa, cikin shekaru 10 da suka gabata, an samu wasu manyan nasarori 3 masu matukar muhimmanci, wandada suka shiga tarihin JKS da al’ummar kasar.

Xi Jinping ya bayyana yayin bude babban taron mambobin JKS karo na 20 cewa, “Mun cika shekaru 100 da kafuwar JKS, gami da mun shiga wani sabon zamani na gurguzu mai sigar kasar Sin, kuma mun fatattaki kangin talauci baki daya, kana mun kammala ginin al’umma mai matsakaicin ci gaba ta kowanne bangare, wato dai, mun cika burinmu na farko a lokacin da muke murnar cika shekaru 100 da kafuwar JKS.”

  • Xi Ya Mika Sakon Alhini Ga Buhari Game Da Hadarin Nutsewar Jirgin Ruwa Da Ya Auku A Kasar

A cewarsa, wadannan muhimman nasarori ne da suka shiga tarihi, nasarorin da JKS da al’ummar Sinawa suka yi namijin kokarin cimmawa cikin hadin kai, kuma nasarorin da za su kasance cikin tarihin kasar har abada, wadanda kuma za su yi gagarumin tasiri ga duniya.

ADVERTISEMENT

Baya ga haka, shugaban kasar Xi Jinping ya yi kira ga dukkan mambobin JKS da su himmantu cikin hadin kai, wajen tabbatar da gina kasar Sin mai tsarin gurguzu ta zamani ta kowacce fuska.

Xi Jinping ya ce taron ya zo ne a lokaci mai muhimmanci, kasancewar jam’iyyar da daukacin Sinawa daga dukkan kabilu, na kan wata sabuwar hanya ta gina kasar zuwa ta zamani mai bin tsarin gurguzu ta kowacce fuska, da kuma kokarin cimma buri na biyu lokacin da za a yi murnar cika shekaru 100 da kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Taken taron shi ne, daukaka tsarin gurguzu mai sigar kasar Sin da aiwatar da tunanin gurguzu mai sigar kasar Sin a sabon zamani da ci gaba da daukaka babban ruhin da jam’iyyar ta kafu a kai da kasancewa cikin kwarin gwiwa da karin karfi, da daukaka muhimman ka’idojin jam’iyyar da samun sabbin nasarori da ci gaba da tabbatar da karfi da kuzarinta da himmantuwa cikin hadin kai wajen gina kasa ta zamani mai bin tsarin gurguzu ta kowacce fuska, tare da kara farfado da kasar ta kowanne bangare.

Cikin rahoton da ya gabatar a yayin bikin bude babban taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya kuma ce JKS za ta aiwatar da dukkanin manuofi da za su ba da damar warware batun yankin Taiwan a sabon zamani, tare da tabbatar da cimma burin dinkewar sassan kasa.

Shugaba Xi ya ce warware batun Taiwan harka ce ta kasar Sin, wadda ya zama wajibi Sin din ta magance ta. Ya ce “Za mu ci gaba da yin aiki tukuru, domin warware wannan batu cikin lumana bisa gaskiya da kwazon aiki, amma ba za mu alkawarta kore yiwuwar amfani da karfi ba, kana muna da nufin duba yiwuwar daukar dukkanin matakai.

Ya kamata masu kokarin tsoma baki na waje, da kuma masu burin ballewar yankin Taiwan da dukkanin ayyukansu su san haka. Ban ambaci hakan domin ’yan uwan mu na Taiwan ba”.

Ban da wannan kuma, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bayyana yayin bude taron mambobin JKS karo na 20 a yau Lahadi cewa, kasarsa ba za ta taba neman yi wa kasashen duniya babakere ko fadada iko da yankunanta ba.

A cewarsa, kasar Sin ta tsaya ne tsayin daka, wajen adawa da duk wani nau’i na babakere da neman iko da yakin cacar baka da tsoma baki cikin harkokin gidan kasashe da kuma nuna fuska biyu. (Masu fassara: Saminu Alhassan, Fa’iza Mustapha)

Xi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu
Daga Birnin Sin

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Next Post
2023: Ba Za Mu Zabi Shugaban Da Ba Zai Mayar Da Hankali Kan Hakkokinmu Ba —’Yan Fansho

EFCC Ta Cafke Ma'aikatan Banki 12 Kan Zargin Satar Kuɗaɗe A Enugu

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.