• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Hukumar Sufuri ta Jihar Zamfara ta kama manyan motoci 50 da ke jigilar kayan abinci daga kasar nan za su shiga Jamhuriyar Nijar.

Hukumar, wacce ke aiwatar da umarnin shugaban kasa da ke da nufin kawo karshen matsalar karancin abinci da tara kaya, ta hana motocin da ke cike da hatsi iri-iri fita daga kasar.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Ina Iya Kera Na’urorin Da Suka Fi Na Kasashen Waje Inganci, In ji Adam

Idan ba a manta ba a ranar Alhamis din da ta gabata Shugaban Kasa Bola Tinubu ya umurci manyan jami’ai uku da suka hada da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro Nuhu Ribadu, da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda Kayode Egbetokun da kuma Babban Daraktan Ma’aikatar Harkokin Gwamnati Yusuf Bichi da su hada kai da gwamnonin jahohi domin ganin an dakile mummunar dabi’ar nan boye kayan abinci.

An dauki matakin ne a yayin ganawar da shugaban kasar ya yi da gwamnonin a Abuja kan matsalar karancin abinci da ake fama da ita a halin yanzu sakamakon hauhawar farashin man fetur bayan cire tallafi da kuma rashin isasshiyar noma saboda ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

A ranar Lahadin da ta gabata ne Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta ce ta dakatar da tireloli 15 da ke jigilar kayan abinci ta kan iyakokin Sokoto zuwa Jamhuriyar Nijar.

Kazalika, gwamnatin Jihar Kano ta rufe rumfunan ajiya guda 10 da aka ce suna tara kayan abinci.

Da yake tabbatar da kama manyan motocin guda 50 a Zamfara, Shehu Sani, dan asalin garin Zurmi da ke Karamar Hukumar Zurmi a jihar, ya shaida wa wani wakilinmu ta wayar tarho a ranar Litinin da ta gabata cewa, an tare motocin ne a Kauyen Gidan Jaja, kusa da garin. Wanda ke kan iyakar Nieriya da Jamhuriyar Nijar.

Kakakin ZARTO, Sale Shinkafi, ya yi zargin cewa manyan motocin na yunkurin safarar kayayyakin abinci ne zuwa Jamhuriyar Nijar.

Ya ce, “Mutanenmu sun tare motoci 50 makil da hatsi iri-iri a lokacin da suke kokarin fitar da su daga kasar. Mun umurci masu su koma su sayar wa ‘yan Nijeriya kayayyakin a kan farashin da ya dace.”

Shinkafi ya bayyana cewa motocin ba su da rakiyar jami’an hukumar amma an umurce su ne kawai su koma yankunansu su sayar da kayayyakin a farashi mai sauki.

Ya ce, “Kun san cewa babban abin da ke damunmu shi ne mu tabbatar da cewa ba a fitar da kayan abinci daga kasar nan ta barauniyar hanya ba. Mun ki ba su damar shiga Jamhuriyar Nijar ne kawai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

Next Post

An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

2 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

16 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

16 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

17 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

18 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

20 hours ago
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.