• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

byIdris Aliyu Daudawa
2 years ago
Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Hukumar Sufuri ta Jihar Zamfara ta kama manyan motoci 50 da ke jigilar kayan abinci daga kasar nan za su shiga Jamhuriyar Nijar.

Hukumar, wacce ke aiwatar da umarnin shugaban kasa da ke da nufin kawo karshen matsalar karancin abinci da tara kaya, ta hana motocin da ke cike da hatsi iri-iri fita daga kasar.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Ina Iya Kera Na’urorin Da Suka Fi Na Kasashen Waje Inganci, In ji Adam

Idan ba a manta ba a ranar Alhamis din da ta gabata Shugaban Kasa Bola Tinubu ya umurci manyan jami’ai uku da suka hada da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro Nuhu Ribadu, da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda Kayode Egbetokun da kuma Babban Daraktan Ma’aikatar Harkokin Gwamnati Yusuf Bichi da su hada kai da gwamnonin jahohi domin ganin an dakile mummunar dabi’ar nan boye kayan abinci.

An dauki matakin ne a yayin ganawar da shugaban kasar ya yi da gwamnonin a Abuja kan matsalar karancin abinci da ake fama da ita a halin yanzu sakamakon hauhawar farashin man fetur bayan cire tallafi da kuma rashin isasshiyar noma saboda ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

A ranar Lahadin da ta gabata ne Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta ce ta dakatar da tireloli 15 da ke jigilar kayan abinci ta kan iyakokin Sokoto zuwa Jamhuriyar Nijar.

Kazalika, gwamnatin Jihar Kano ta rufe rumfunan ajiya guda 10 da aka ce suna tara kayan abinci.

Da yake tabbatar da kama manyan motocin guda 50 a Zamfara, Shehu Sani, dan asalin garin Zurmi da ke Karamar Hukumar Zurmi a jihar, ya shaida wa wani wakilinmu ta wayar tarho a ranar Litinin da ta gabata cewa, an tare motocin ne a Kauyen Gidan Jaja, kusa da garin. Wanda ke kan iyakar Nieriya da Jamhuriyar Nijar.

Kakakin ZARTO, Sale Shinkafi, ya yi zargin cewa manyan motocin na yunkurin safarar kayayyakin abinci ne zuwa Jamhuriyar Nijar.

Ya ce, “Mutanenmu sun tare motoci 50 makil da hatsi iri-iri a lokacin da suke kokarin fitar da su daga kasar. Mun umurci masu su koma su sayar wa ‘yan Nijeriya kayayyakin a kan farashin da ya dace.”

Shinkafi ya bayyana cewa motocin ba su da rakiyar jami’an hukumar amma an umurce su ne kawai su koma yankunansu su sayar da kayayyakin a farashi mai sauki.

Ya ce, “Kun san cewa babban abin da ke damunmu shi ne mu tabbatar da cewa ba a fitar da kayan abinci daga kasar nan ta barauniyar hanya ba. Mun ki ba su damar shiga Jamhuriyar Nijar ne kawai.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version