An daddale yarjejeniyoyi masu tarin yawa a yayin taron baje kolin harkokin tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afirka karo na hudu da aka kammala jiya Lahadi 15 ga watan nan, a gabar da sassan biyu ke kara zurfafa hadin gwiwarsu.
Kwamitin tsara baje kolin ya sanar da cewa, an sanya hannu kan yarjejeniyoyi na gudanar da ayyuka 176 da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 11.39. Alkaluman karuwar adadin ayyukan da aka amince za a aiwatar sun karu da kaso 45.8 bisa dari, yayin da na kudaden gudanar da ayyukan suka karu da kaso 10.6 bisa dari kan na shekarar 2023.
Ya zuwa tsakar ranar jiyan, sama da mutane 200,000 sun ziyarci harabar baje kolin da aka kammala a birnin Changsha, fadar mulkin lardin Hunan na tsakiyar kasar Sin, adadin da ya rubanya wanda aka gani a taron da ya gabaci na bana.
Har ila yau a karon farko, baje kolin ya kunshi nune-nunen hajojin hadin gwiwar kamfanonin Sin da na kasashen Afirka, da kayayyaki masu inganci na Afirka, da kayayyakin kawa na masana’antun Sin da Afirka.
Kusan kamfanoni 2,100, da suka hada da 764 daga kasashen Afika 43 ne suka halarci baje kolin. Yayin da masu sayayya daga Sin da sauran sassan kasa da kasa 12,000 suka halarci bikin.
Kazalika, cikin kwanaki hudu da aka kwashe ana gudanar da baje kolin, an sayar da nau’o’in albarkatun gona na nahiyar Afirka sama da 200 ta intanet da kuma manyan shaguna. Bugu da kari, wasu kasashen Afirka 14 sun gudanar da wasu ayyukan musamman na yayata hada-hadar tattalin arziki da cinikayya a yayin baje kolin. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp