• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

by Idris Umar
2 months ago
Zariya

Bayan kwana shida ana ci gaba da neman gawarta, a ƙarshe an gano gawar yarinya Haneefa, mai shekaru uku, wadda ruwan sama ya tafi da ita a Zariya. An gano gawar ce da safiyar Lahadi, a bayan Gyallesu, ƙasan Kilaco, kamar yadda babban jami’in Red Cross na shiyyar Zariya, Abdulmumin Adamu, ya tabbatar.

A cewarsa, wannan ya kawo ƙarshen binciken neman waɗanda iftila’in ambaliyar ruwan sama ya rutsa da su. A ranar 8 ga Satumba 2025, ruwan sama mai ƙarfi da aka tafka a unguwar Tudun Jukun kusa da Tukur-Tukur ya yi sanadin mutuwar Fatima Sani Danmarke da Yusuf Surajo (wanda aka fi sani da Abba), wanda sun kasance duk ɗalibai ne, tare da janyo ɓacewar Haneefa wadda Fatima ke goye da ita a lokacin.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
  • Jam’iyyar APC Ta Lashe Zaɓen Kujerun ‘Yan Majalisun Zariya Da Basawa

Kakan yarinyar, Mallam Suleiman, wanda ke zaune a layin Adamu Mai Aljana, Magume, ya tabbatar da cewa wata bishiya ce ta tare gawar yarinyar a bayan Gyallesu. Ya bayyana cewa an gudanar da Sallar jana’iza nan take bayan gano gawar, duk da cewa tun a jiya aka yi mata Salatul Gaib a masallacin Mallam Isa Cikon Kwami.

Dangin yarinyar, ciki har da Alhaji Sani Danmarke, sun yi godiya ga jama’a bisa jajircewa wajen neman yaran da iftila’in ya shafa, tare da yin addu’ar rahma ga mamatan.

A halin yanzu, limaman masallatai na ci gaba da wayar da kan al’umma kan matakan kariya, suna jan hankalin iyaye da masu ababen hawa su yi hattara yayin ruwan sama mai ƙarfi, don guje wa maimaituwar irin wannan masifa.

LABARAI MASU NASABA

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo
Manyan Labarai

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 
Manyan Labarai

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Next Post
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

LABARAI MASU NASABA

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.