ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Gwamnati

Kungiyar Likitan Gwamnati Masu Koyon Aiki (NARD) ta zargi Gwamnatin Tarayya da yaɗa bayanan da ba gaskiya ba game da halin da ake ciki kan walwalar likitoci da sauye-sauyen da ake iƙirarin ana yi a fannin lafiya.

A wata sanarwa da Shugaban NARD, Dr. Mohammad Suleiman, tare da Sakataren Janar, Dr. Shuaibu Ibrahim, da Sakataren Yaɗa Labarai, Dr. Abdulmajid Ibrahim suka sanya hannu a ranar Litinin, ƙungiyar ta bayyana cewa bayanan da ma’aikatar lafiya ta fitar “ƙirƙirarran labari ne wanda ba gaskiya ba,” yayin da asibitoci na gwamnati ke ci gaba da durƙushewa saboda rashin kulawa da alƙawurran gwamnati.

  • Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo
  • Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Ƙungiyar ta soki sanarwar da Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya ta fitar a ranar 31 ga Oktoba, inda ta bayyana cewa an yi nufin ruɗar da jama’a ne. NARD ta roƙi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya binciki gaskiyar lamuran da kansa, maimakon dogaro da rahotannin da aka ƙawata. Ta ce akwai buƙatun su 19 da ba a cika ba, ciki har da biyan bashin albashi da alawus-alawus, da ƙarin kashi 25/35 cikin 100 na CONMESS, da sauran haƙƙoƙi da suka daɗe sama da shekaru biyar ba a biya ba.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyar ta ƙaryata iƙirarin cewa gwamnati ta saki biliyan ₦30 biliyan domin biyan bashin da aka tarawa likitoci, tana mai cewa mafi yawan mambobinta ba su ga ko sisi ba. NARD ta kuma soki tsarin IPPIS, tana cewa shi ne ke haifar da matsalolin ragin albashi da jinkirin biyan kuɗi, tare da kiran a samar da sabuwar hanya ta musamman ta ma’aikatan lafiya.

Haka kuma, ta yi watsi da iƙirarin cewa an ɗauki sabbin ma’aikatan lafiya dubu 20, tana mai cewa adadin likitocin gwamnati ya ragu daga 16,000 zuwa kimanin 9,000 cikin shekaru goma saboda rashin walwala da haɗarin aiki.

LABARAI MASU NASABA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

Ko da yake ƙungiyar ta yaba da sakin biliyan ₦10.6 ga asusun gidauniyar likitoci masu neman ƙwarewa (Medical Residency Training Fund) (MRTF) na 2025, ta ce biyan ya kamata ya zama na yau da kullum, a buɗe, kuma ya dace da hauhawar farashi.

NARD ta kuma yi tir da dawo da wasu daga cikin likitocin da aka kora a Asibitin Koyarwa na Lokoja (FTH Lokoja), tana mai cewa dole ne a dawo da dukkan su ba tare da sharaɗi ba. Sauran matsalolin da ta jero sun haɗa da bashin albashi da ba a biya ba a BSUTH, da FMC Owo, da OAUTHC Ile-Ife, rashin aiwatar da tsarin one-for-one replacement, da kuma matsalar amfani da likitoci ƴan kwangila a asibitoci da dama.

NARD ta jaddada cewa tana shirye ta ci gaba da tattaunawa, amma ta ce yajin aikin da ake yi yanzu ba domin cutar da ƴan Nijeriya ba ne, sai domin ceto tsarin lafiya da ke gab da rugujewa. “Yaƙinmu ba na neman kuɗi kawai ba ne, sai na tsira da mutunci, da tsaro, da rayuwa cikin aminci,” in ji sanarwar.

Gwamnati
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya
  • Abubakar Sulaiman
    Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki
  • Abubakar Sulaiman
    Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

MASU ALAKA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin
Manyan Labarai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

June 14, 2026
Next Post
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

LABARAI MASU NASABA

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

June 14, 2026
Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.