ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, September 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Gwamnati

Kungiyar Likitan Gwamnati Masu Koyon Aiki (NARD) ta zargi Gwamnatin Tarayya da yaɗa bayanan da ba gaskiya ba game da halin da ake ciki kan walwalar likitoci da sauye-sauyen da ake iƙirarin ana yi a fannin lafiya.

A wata sanarwa da Shugaban NARD, Dr. Mohammad Suleiman, tare da Sakataren Janar, Dr. Shuaibu Ibrahim, da Sakataren Yaɗa Labarai, Dr. Abdulmajid Ibrahim suka sanya hannu a ranar Litinin, ƙungiyar ta bayyana cewa bayanan da ma’aikatar lafiya ta fitar “ƙirƙirarran labari ne wanda ba gaskiya ba,” yayin da asibitoci na gwamnati ke ci gaba da durƙushewa saboda rashin kulawa da alƙawurran gwamnati.

  • Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo
  • Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Ƙungiyar ta soki sanarwar da Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya ta fitar a ranar 31 ga Oktoba, inda ta bayyana cewa an yi nufin ruɗar da jama’a ne. NARD ta roƙi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya binciki gaskiyar lamuran da kansa, maimakon dogaro da rahotannin da aka ƙawata. Ta ce akwai buƙatun su 19 da ba a cika ba, ciki har da biyan bashin albashi da alawus-alawus, da ƙarin kashi 25/35 cikin 100 na CONMESS, da sauran haƙƙoƙi da suka daɗe sama da shekaru biyar ba a biya ba.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyar ta ƙaryata iƙirarin cewa gwamnati ta saki biliyan ₦30 biliyan domin biyan bashin da aka tarawa likitoci, tana mai cewa mafi yawan mambobinta ba su ga ko sisi ba. NARD ta kuma soki tsarin IPPIS, tana cewa shi ne ke haifar da matsalolin ragin albashi da jinkirin biyan kuɗi, tare da kiran a samar da sabuwar hanya ta musamman ta ma’aikatan lafiya.

Haka kuma, ta yi watsi da iƙirarin cewa an ɗauki sabbin ma’aikatan lafiya dubu 20, tana mai cewa adadin likitocin gwamnati ya ragu daga 16,000 zuwa kimanin 9,000 cikin shekaru goma saboda rashin walwala da haɗarin aiki.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Fintiri, Dangote Da Sarakunan Gargajiya Sun Halarci Jana’izar Bamanga Tukur A Yola

Tsohon Kwamishina A Gombe, Ya Marawa Pantami Baya

Ko da yake ƙungiyar ta yaba da sakin biliyan ₦10.6 ga asusun gidauniyar likitoci masu neman ƙwarewa (Medical Residency Training Fund) (MRTF) na 2025, ta ce biyan ya kamata ya zama na yau da kullum, a buɗe, kuma ya dace da hauhawar farashi.

NARD ta kuma yi tir da dawo da wasu daga cikin likitocin da aka kora a Asibitin Koyarwa na Lokoja (FTH Lokoja), tana mai cewa dole ne a dawo da dukkan su ba tare da sharaɗi ba. Sauran matsalolin da ta jero sun haɗa da bashin albashi da ba a biya ba a BSUTH, da FMC Owo, da OAUTHC Ile-Ife, rashin aiwatar da tsarin one-for-one replacement, da kuma matsalar amfani da likitoci ƴan kwangila a asibitoci da dama.

NARD ta jaddada cewa tana shirye ta ci gaba da tattaunawa, amma ta ce yajin aikin da ake yi yanzu ba domin cutar da ƴan Nijeriya ba ne, sai domin ceto tsarin lafiya da ke gab da rugujewa. “Yaƙinmu ba na neman kuɗi kawai ba ne, sai na tsira da mutunci, da tsaro, da rayuwa cikin aminci,” in ji sanarwar.

Gwamnati
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
  • Abubakar Sulaiman
    Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN
  • Abubakar Sulaiman
    Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

MASU ALAKA

Gwamna Fintiri, Dangote Da Sarakunan Gargajiya Sun Halarci Jana’izar Bamanga Tukur A Yola
Manyan Labarai

Gwamna Fintiri, Dangote Da Sarakunan Gargajiya Sun Halarci Jana’izar Bamanga Tukur A Yola

September 13, 2026
Tsohon Kwamishina A Gombe, Ya Marawa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Kwamishina A Gombe, Ya Marawa Pantami Baya

September 13, 2026
Zan Yi Amfani Da Dukiyata Wajen Samun Nasarar Gwamnan Jihar Kano A 2027 – Amb Adesuwa
Manyan Labarai

Zan Yi Amfani Da Dukiyata Wajen Samun Nasarar Gwamnan Jihar Kano A 2027 – Amb Adesuwa

September 13, 2026
Next Post
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

LABARAI MASU NASABA

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Gwamnati

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Gwamnati

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Gwamnati

An Gudanar Da Sallar Zana’idar Tsohon Gwamnan Gongola

September 13, 2026
Yajin Aikin ASUU: Malaman Jami’ar Jihar Kaduna Sun Bijirewa El-rufa’i

Gwamna Uba Sani Ya Amince Da Ƙarin Albashi Ga Ma’aikatan KASU

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.