• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Yadda Ake Amfani Da Jiragen Sama Masu Zaman Kansu Wajen Haramtacciyar Harƙyalla

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Jiragen sama

Ministan sufurin jiragen sama na ƙasa Festus Keyamo, SAN, ya fitar da wata sanarwa dangane da ayyukan da jiragen sama masu zaman kansu ke yi a Nijeriya ba tare da bin ƙa’ida ba, yana mai nuna damuwarsu kan shigarsu cikin haramtattun ayyuka kamar safarar kuɗi haramun da safarar miyagun kwayoyi.

Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin mai mambobi takwas a Abuja, Keyamo ya jaddada buƙatar yin gaggawar daƙile waɗannan ayyuka. Ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da kwamitin zai taka wajen sanya al’umma su sake amince wa da su a fannin sufurin jiragen sama, da tabbatar da bin ƙa’idojin tsaro, da kuma kawar da ayyukan da ba su dace ba.

  • Jirgin Ƙasan Abuja – Kaduna Ya Sake Kauce Hanya
  • Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

Sabon kwamitin da aka kafa ƙarƙashin jagorancin Kaftin Ado Sanusi, ana so ne ya gudanar da cikakkiyar ƙididdigar jirage masu zaman kansu da ba na kasuwanci ba da kuma bincikar ayyukan masu ɗauke da takardar shaidar amfani da sararin samaniya (AOC).

Har ila yau aikin kwamitin ya haɗa da binciken dalilin da yasa jiragen haya ba bisa ƙa’ida ba suka ci gaba da kasancewa a Nijeriya duk da ƙa’idojin da ake da su da kuma tabbatar da sahihancin ma’aikatan jirgi masu lasisi da na bogi.

Bugu da ƙari, an ba wa kwamitin ikon bayar da ingantattun shawarwari don ɗaukar matakai da nufin daƙile ayyukan jirge marasa izini da kuma inganta sa ido kan jiragen sama masu zaman kansu a duk faɗin ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

A jawabinsa, Kyaftin Sanusi ya ce, a matsayinsa na shugaban kwamitin, ya nuna jin daɗinsa da damar da aka ba shi na magance waɗannan muhimman batutuwa. Ya tabbatar da ƙudirin kwamitin na yin bincike kan musabbabin ayyukan da suka shafi jiragen sama masu zaman kansu da kuma samar da tsauraran matakai da za su kare mutunci da tsaron sararin samaniyar Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Next Post
Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya

Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.