• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Yadda Ake Amfani Da Jiragen Sama Masu Zaman Kansu Wajen Haramtacciyar Harƙyalla

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
An Gano Yadda Ake Amfani Da Jiragen Sama Masu Zaman Kansu Wajen Haramtacciyar Harƙyalla
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan sufurin jiragen sama na ƙasa Festus Keyamo, SAN, ya fitar da wata sanarwa dangane da ayyukan da jiragen sama masu zaman kansu ke yi a Nijeriya ba tare da bin ƙa’ida ba, yana mai nuna damuwarsu kan shigarsu cikin haramtattun ayyuka kamar safarar kuɗi haramun da safarar miyagun kwayoyi.

Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin mai mambobi takwas a Abuja, Keyamo ya jaddada buƙatar yin gaggawar daƙile waɗannan ayyuka. Ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da kwamitin zai taka wajen sanya al’umma su sake amince wa da su a fannin sufurin jiragen sama, da tabbatar da bin ƙa’idojin tsaro, da kuma kawar da ayyukan da ba su dace ba.

  • Jirgin Ƙasan Abuja – Kaduna Ya Sake Kauce Hanya
  • Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

Sabon kwamitin da aka kafa ƙarƙashin jagorancin Kaftin Ado Sanusi, ana so ne ya gudanar da cikakkiyar ƙididdigar jirage masu zaman kansu da ba na kasuwanci ba da kuma bincikar ayyukan masu ɗauke da takardar shaidar amfani da sararin samaniya (AOC).

Har ila yau aikin kwamitin ya haɗa da binciken dalilin da yasa jiragen haya ba bisa ƙa’ida ba suka ci gaba da kasancewa a Nijeriya duk da ƙa’idojin da ake da su da kuma tabbatar da sahihancin ma’aikatan jirgi masu lasisi da na bogi.

Bugu da ƙari, an ba wa kwamitin ikon bayar da ingantattun shawarwari don ɗaukar matakai da nufin daƙile ayyukan jirge marasa izini da kuma inganta sa ido kan jiragen sama masu zaman kansu a duk faɗin ƙasar.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

A jawabinsa, Kyaftin Sanusi ya ce, a matsayinsa na shugaban kwamitin, ya nuna jin daɗinsa da damar da aka ba shi na magance waɗannan muhimman batutuwa. Ya tabbatar da ƙudirin kwamitin na yin bincike kan musabbabin ayyukan da suka shafi jiragen sama masu zaman kansu da kuma samar da tsauraran matakai da za su kare mutunci da tsaron sararin samaniyar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AirportFestus KeyamoJirgiPlanePrivate Jet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Zargi Amurka Da Kitsa Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Next Post

Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya

Related

Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 minutes ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

1 hour ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

2 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

5 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

5 hours ago
Next Post
Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya

Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya

LABARAI MASU NASABA

Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.