ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Kan “Kara Zurfafa Gyare-gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya” Da Kuma Musayar Jama’a Tsakanin Sin Da Masar Na Shekarar Hadin Gwiwa 

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Sin

An gudanar da taron tattaunawa kan “Kara zurfafa gyare-gyare a Sin dama ce ga duniya” da kuma musayar jama’a tsakanin Sin da Masar na shekarar hadin gwiwa a Cairo, babban birnin Masar, a jiya Talata bisa agogon wurin, wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG, da ma’aikatar yawon shakatawa da kayayyakin tarihi ta kasar Masar, da kuma ofishin jakadancin kasar Sin dake Masar suka gudanar tare.

 

A gun taron, baki daga kasashen Sin da Masar sun yi mu’amala mai zurfi da juna kan damar samun ci gaba ga duniya, sakamakon kara zurfafa gyare-gyare a Sin a sabon zamani. Ban da haka, an watsa wani shirin da CMG ya kaddamar mai taken “Sabon nau’i na wayewar dan Adam:Salon zamanintar da kasar Sin” da harshen Larabci a kasar Masar, kuma a ranar har ila yau, an kuma kaddamar da ayyuka da dama a fannonin fina-finai da shirye-shiryen talabijin, da kafofin watsa labarai da kuma al’adu.

ADVERTISEMENT

 

Shen Haixiong, mataimakin shugaban hukumar fadakar da al’umma na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban CMG, ya bayyana cewa, Sin ta kara zurfafa gyare-gyare a kasar, ko shakka babu, zai samar da tabbaci mai kima a cikin duniya mai cike da rudani, da kuma samar da karin damammakin samun ci gaba, da kara kuzarin Sin ga inganta ci gaba da wadatar bil’adama tare. CMG zai yi amfani da taron tattaunawa da musaya tsakanin jama’a na wannan karo a matsayin mafari don kara karfafa mu’amala da hadin gwiwa, da zurfafa fahimtar juna kan wayewar kai, da karfafa da fadada hadin gwiwa mai inganci tsakanin kasashen biyu a fannonin zurfafa gyare-gyare da mu’amalar al’adu tare da bangarori daban daban na Masar, ta yadda za a ba da gudummawar hikima da karfi ga gina al’ummar mai makomar bai daya ta Sin da Masar da al’ummar mai makomar bai daya ta Sin da kasashen Larabawa a sabon zamani. (Safiyah Ma)

LABARAI MASU NASABA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95
Daga Birnin Sin

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
Next Post
ECOWAS Ta Bada Tallafin Kayan Abinci Ga Mutane 12,000 Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Adamawa

ECOWAS Ta Bada Tallafin Kayan Abinci Ga Mutane 12,000 Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.