• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Ficewar Sojojin Amurka Daga Nijar A Hukumance

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
An Kaddamar Da Ficewar Sojojin Amurka Daga Nijar A Hukumance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi bikin kaddamar da ayyukan kwashe sojojin Amurka a hukumance da yammacin a filin jirgin sojin sama da ke Birnin Yamai na Jamhiriyyar Nijar.

Tsarin jadawalin da tawwagar jami’an Pentagon ta cimma matsaya a kansa tare da jami’an ma’aikatar tsaron Nijar a ranar 19 ga watan Mayun da ya gabata, shi ne ya kayyade cewa za a ci gaba da ayyukan kwashe dakarun na Amurka har zuwa ranar 15 ga watan Satumba, 2024 a matsayin wa’adin karshe.

  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara
  • Jamus Za Ta Bar Sansanin Sojinta Na Nijar A Bude Bisa Yarjejeniyar Wucin Gadi

Jami’in Ma’aikatar Pentagon Janar Kenneth Ekman ya yi jawabi a yayin kwarya-kwaryar bikin da aka shirya a filin jirgin sojan saman base 101 da aka fi sani da Escadrille wanda ke matsayin sansanin da kasashe aminnan Nijar suka kwashe kayan ayyukan dakarunsu, inda shi ne aka kaddamar da ayyukan fice-war sojan Amurka daga Nijer.

Tun ranar 16 ga watan Maris, 2024 da hukumomin mulkin sojan Nijar suka ba da sanarwar yanke huldar ayyukan soji da Amurka sakamakon abin da suka ki-ra rashin halaccin yarjejeniyar da kasashen biyu suka rattabawa hannu a she-karar 2012 da nufin karfafa matakan yaki da ta’addanci.

A ranar 19 ga watan Mayun 2024 ne Amurka da Nijer suka amince da tsarin jadawalin kwashe dakaru 1000 da ‘yan kai da Amurka ta girke a wannan Nijar.

Labarai Masu Nasaba

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

Colonel Major Maman Sani KIAOU shi ne babban kwamandan rundunar sojan kasa, ya ce daga ranar 19 ga watan Mayu dakaru 269 aka kwashe daga ci-kin 946 da ton-ton na kayan aiki da ake shirin ficewa da su daga Nijer saboda haka a wannan karon jirgin sojan Amurka samfarin C 17 GLOBMASTER III zai daga da wani rukuni na wadanan dakaru.

Domin gudanar da ayyukan cikin sauki da fahimta an kafa wani kwamitin had-in gwiwa wanda ya bullo da tsarin da za a tafiyar da lamuran da suka shafi sha’anin ba da izinin sauka da tashin jirage da ratsa sararin samaniya yadda ya kamata, kuma ayarin motocin sojojin Amurka sun tashi daga Ouallam da Diffa zuwa Yamai da Agadez.

Dangane da abubuwan da aka tsayar a yarjejeniyar ta ranar 19 ga watan Mayun 2024 bangarorin sun yi na’am da bukatar inda wasu kwararun sojojin Amurka da za su yi aikin tattara kayayaki a sansanin sojan sama na 101 da ke Yamai da sansani na 201 dake yankin Agadez.

Kafin ranar 15 ga watan Satumban dake tafe ne ya kamata sojojin Amurka su kammala ficewa gaba daya daga Nijar kamar yadda hukumomi suka nuna bukata, matakin da ya sami goyon baya daga mafi yawancin al’ummar kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GermanyJamusNigerNijar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sallah: Tinubu Ya Bukaci Hadin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin ‘Yan Nijeriya

Next Post

Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Related

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

6 days ago
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu
Kasashen Ketare

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

1 week ago
Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine
Kasashen Ketare

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

2 weeks ago
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari
Kasashen Ketare

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

2 weeks ago
Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

2 weeks ago
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka
Kasashen Ketare

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

2 weeks ago
Next Post
Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.