• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Ficewar Sojojin Amurka Daga Nijar A Hukumance

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
An Kaddamar Da Ficewar Sojojin Amurka Daga Nijar A Hukumance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi bikin kaddamar da ayyukan kwashe sojojin Amurka a hukumance da yammacin a filin jirgin sojin sama da ke Birnin Yamai na Jamhiriyyar Nijar.

Tsarin jadawalin da tawwagar jami’an Pentagon ta cimma matsaya a kansa tare da jami’an ma’aikatar tsaron Nijar a ranar 19 ga watan Mayun da ya gabata, shi ne ya kayyade cewa za a ci gaba da ayyukan kwashe dakarun na Amurka har zuwa ranar 15 ga watan Satumba, 2024 a matsayin wa’adin karshe.

  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara
  • Jamus Za Ta Bar Sansanin Sojinta Na Nijar A Bude Bisa Yarjejeniyar Wucin Gadi

Jami’in Ma’aikatar Pentagon Janar Kenneth Ekman ya yi jawabi a yayin kwarya-kwaryar bikin da aka shirya a filin jirgin sojan saman base 101 da aka fi sani da Escadrille wanda ke matsayin sansanin da kasashe aminnan Nijar suka kwashe kayan ayyukan dakarunsu, inda shi ne aka kaddamar da ayyukan fice-war sojan Amurka daga Nijer.

Tun ranar 16 ga watan Maris, 2024 da hukumomin mulkin sojan Nijar suka ba da sanarwar yanke huldar ayyukan soji da Amurka sakamakon abin da suka ki-ra rashin halaccin yarjejeniyar da kasashen biyu suka rattabawa hannu a she-karar 2012 da nufin karfafa matakan yaki da ta’addanci.

A ranar 19 ga watan Mayun 2024 ne Amurka da Nijer suka amince da tsarin jadawalin kwashe dakaru 1000 da ‘yan kai da Amurka ta girke a wannan Nijar.

Labarai Masu Nasaba

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

Colonel Major Maman Sani KIAOU shi ne babban kwamandan rundunar sojan kasa, ya ce daga ranar 19 ga watan Mayu dakaru 269 aka kwashe daga ci-kin 946 da ton-ton na kayan aiki da ake shirin ficewa da su daga Nijer saboda haka a wannan karon jirgin sojan Amurka samfarin C 17 GLOBMASTER III zai daga da wani rukuni na wadanan dakaru.

Domin gudanar da ayyukan cikin sauki da fahimta an kafa wani kwamitin had-in gwiwa wanda ya bullo da tsarin da za a tafiyar da lamuran da suka shafi sha’anin ba da izinin sauka da tashin jirage da ratsa sararin samaniya yadda ya kamata, kuma ayarin motocin sojojin Amurka sun tashi daga Ouallam da Diffa zuwa Yamai da Agadez.

Dangane da abubuwan da aka tsayar a yarjejeniyar ta ranar 19 ga watan Mayun 2024 bangarorin sun yi na’am da bukatar inda wasu kwararun sojojin Amurka da za su yi aikin tattara kayayaki a sansanin sojan sama na 101 da ke Yamai da sansani na 201 dake yankin Agadez.

Kafin ranar 15 ga watan Satumban dake tafe ne ya kamata sojojin Amurka su kammala ficewa gaba daya daga Nijar kamar yadda hukumomi suka nuna bukata, matakin da ya sami goyon baya daga mafi yawancin al’ummar kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GermanyJamusNigerNijar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sallah: Tinubu Ya Bukaci Hadin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin ‘Yan Nijeriya

Next Post

Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Related

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya
Kasashen Ketare

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

3 hours ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Kasashen Ketare

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

6 days ago
Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan
Kasashen Ketare

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

2 weeks ago
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi
Kasashen Ketare

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

2 weeks ago
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida
Kasashen Ketare

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

3 weeks ago
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

3 weeks ago
Next Post
Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.