• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Ficewar Sojojin Amurka Daga Nijar A Hukumance

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Sojojin

An yi bikin kaddamar da ayyukan kwashe sojojin Amurka a hukumance da yammacin a filin jirgin sojin sama da ke Birnin Yamai na Jamhiriyyar Nijar.

Tsarin jadawalin da tawwagar jami’an Pentagon ta cimma matsaya a kansa tare da jami’an ma’aikatar tsaron Nijar a ranar 19 ga watan Mayun da ya gabata, shi ne ya kayyade cewa za a ci gaba da ayyukan kwashe dakarun na Amurka har zuwa ranar 15 ga watan Satumba, 2024 a matsayin wa’adin karshe.

  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara
  • Jamus Za Ta Bar Sansanin Sojinta Na Nijar A Bude Bisa Yarjejeniyar Wucin Gadi

Jami’in Ma’aikatar Pentagon Janar Kenneth Ekman ya yi jawabi a yayin kwarya-kwaryar bikin da aka shirya a filin jirgin sojan saman base 101 da aka fi sani da Escadrille wanda ke matsayin sansanin da kasashe aminnan Nijar suka kwashe kayan ayyukan dakarunsu, inda shi ne aka kaddamar da ayyukan fice-war sojan Amurka daga Nijer.

Tun ranar 16 ga watan Maris, 2024 da hukumomin mulkin sojan Nijar suka ba da sanarwar yanke huldar ayyukan soji da Amurka sakamakon abin da suka ki-ra rashin halaccin yarjejeniyar da kasashen biyu suka rattabawa hannu a she-karar 2012 da nufin karfafa matakan yaki da ta’addanci.

A ranar 19 ga watan Mayun 2024 ne Amurka da Nijer suka amince da tsarin jadawalin kwashe dakaru 1000 da ‘yan kai da Amurka ta girke a wannan Nijar.

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Colonel Major Maman Sani KIAOU shi ne babban kwamandan rundunar sojan kasa, ya ce daga ranar 19 ga watan Mayu dakaru 269 aka kwashe daga ci-kin 946 da ton-ton na kayan aiki da ake shirin ficewa da su daga Nijer saboda haka a wannan karon jirgin sojan Amurka samfarin C 17 GLOBMASTER III zai daga da wani rukuni na wadanan dakaru.

Domin gudanar da ayyukan cikin sauki da fahimta an kafa wani kwamitin had-in gwiwa wanda ya bullo da tsarin da za a tafiyar da lamuran da suka shafi sha’anin ba da izinin sauka da tashin jirage da ratsa sararin samaniya yadda ya kamata, kuma ayarin motocin sojojin Amurka sun tashi daga Ouallam da Diffa zuwa Yamai da Agadez.

Dangane da abubuwan da aka tsayar a yarjejeniyar ta ranar 19 ga watan Mayun 2024 bangarorin sun yi na’am da bukatar inda wasu kwararun sojojin Amurka da za su yi aikin tattara kayayaki a sansanin sojan sama na 101 da ke Yamai da sansani na 201 dake yankin Agadez.

Kafin ranar 15 ga watan Satumban dake tafe ne ya kamata sojojin Amurka su kammala ficewa gaba daya daga Nijar kamar yadda hukumomi suka nuna bukata, matakin da ya sami goyon baya daga mafi yawancin al’ummar kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga
Kasashen Ketare

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Next Post
Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Sojojin

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.