ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Ficewar Sojojin Amurka Daga Nijar A Hukumance

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Sojojin

An yi bikin kaddamar da ayyukan kwashe sojojin Amurka a hukumance da yammacin a filin jirgin sojin sama da ke Birnin Yamai na Jamhiriyyar Nijar.

Tsarin jadawalin da tawwagar jami’an Pentagon ta cimma matsaya a kansa tare da jami’an ma’aikatar tsaron Nijar a ranar 19 ga watan Mayun da ya gabata, shi ne ya kayyade cewa za a ci gaba da ayyukan kwashe dakarun na Amurka har zuwa ranar 15 ga watan Satumba, 2024 a matsayin wa’adin karshe.

  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara
  • Jamus Za Ta Bar Sansanin Sojinta Na Nijar A Bude Bisa Yarjejeniyar Wucin Gadi

Jami’in Ma’aikatar Pentagon Janar Kenneth Ekman ya yi jawabi a yayin kwarya-kwaryar bikin da aka shirya a filin jirgin sojan saman base 101 da aka fi sani da Escadrille wanda ke matsayin sansanin da kasashe aminnan Nijar suka kwashe kayan ayyukan dakarunsu, inda shi ne aka kaddamar da ayyukan fice-war sojan Amurka daga Nijer.

ADVERTISEMENT

Tun ranar 16 ga watan Maris, 2024 da hukumomin mulkin sojan Nijar suka ba da sanarwar yanke huldar ayyukan soji da Amurka sakamakon abin da suka ki-ra rashin halaccin yarjejeniyar da kasashen biyu suka rattabawa hannu a she-karar 2012 da nufin karfafa matakan yaki da ta’addanci.

A ranar 19 ga watan Mayun 2024 ne Amurka da Nijer suka amince da tsarin jadawalin kwashe dakaru 1000 da ‘yan kai da Amurka ta girke a wannan Nijar.

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

Colonel Major Maman Sani KIAOU shi ne babban kwamandan rundunar sojan kasa, ya ce daga ranar 19 ga watan Mayu dakaru 269 aka kwashe daga ci-kin 946 da ton-ton na kayan aiki da ake shirin ficewa da su daga Nijer saboda haka a wannan karon jirgin sojan Amurka samfarin C 17 GLOBMASTER III zai daga da wani rukuni na wadanan dakaru.

Domin gudanar da ayyukan cikin sauki da fahimta an kafa wani kwamitin had-in gwiwa wanda ya bullo da tsarin da za a tafiyar da lamuran da suka shafi sha’anin ba da izinin sauka da tashin jirage da ratsa sararin samaniya yadda ya kamata, kuma ayarin motocin sojojin Amurka sun tashi daga Ouallam da Diffa zuwa Yamai da Agadez.

Dangane da abubuwan da aka tsayar a yarjejeniyar ta ranar 19 ga watan Mayun 2024 bangarorin sun yi na’am da bukatar inda wasu kwararun sojojin Amurka da za su yi aikin tattara kayayaki a sansanin sojan sama na 101 da ke Yamai da sansani na 201 dake yankin Agadez.

Kafin ranar 15 ga watan Satumban dake tafe ne ya kamata sojojin Amurka su kammala ficewa gaba daya daga Nijar kamar yadda hukumomi suka nuna bukata, matakin da ya sami goyon baya daga mafi yawancin al’ummar kasar.

Sojojin
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Sojojin
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Sojojin
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
Sojojin
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da ‘Yan Bindiga

Gwamna Dauda Ya Karrama Askarawan Zamfara 20 Da Ke Nuna Bajinta A Yaki Da 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.