An zabi jimilar wakilai 2,296 da za su halarci babban taron wakilan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 20 dake karatowa.
Wata sanarwa da aka fitar yau, ta ce an zabi wakilan ne bisa kundin tsarin mulkin jam’iyyar, da tanade-tanaden kwamitin koli na jam’iyyar tare da aiwatar da dabarun da kwamitin ke bukata.
A cewar sanarwar, matsayin wakilan shi ne wakilci, bisa tanadin da kwamitin kolin JKS ya gindaya kan adadin wakilai daga bangarori daban daban. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp