• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Dorinar Ruwa A Jihar Kebbi Bayan Ta Kashe Mai-Gadin Lambun Basarake

by Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
An Kashe Dorinar Ruwa A Jihar Kebbi Bayan Ta Kashe Mai-Gadin Lambun Basarake
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu gungun masunta da manoma dauke da baka da kibau sun samu nasarar kashe dorinar ruwa da ta kashe Maigadin sarkin Lambun Sarkin Yauri, Dakta Muhammad Zayyanu Abdullahi tare da raunata wani masunci a kogin Gungun Sarki da ke garin Yauri a jihar Kebbi. Inda a halin yanzu masuncin ke jinya a asibitin koyarwa ta Usmanu Dan fodiyo da ke jihar Sakkwato don kula da lafiyarsa.

 

Gwamnan Jihar, Nasir Idris ne ya bada umurnin ga al’ummar yankin da su fantsama fagen farautar dorinar su kashe ta, sakon hakan ya fito ne ta hannun mai martaba Sarkin Yauri, Dakta Muhammad Zayyanu Abdullahi.

  • Sanata Sani Ya Nemi Tinubu Ya Saki Masu Zanga-zanga Da Ke Tsare
  • Jihar Kogi Ta Amince Da Naira 72,000 Mafi Karancin Albashin Ma’aikata 

A yayin da wakilinmu ya samu zantawa da Alhaji Nasiru Sarki, Mayanan Gungun wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wata hira ta wayar tarho, inda ya bayyana cewa masunta da manoman sun fantsama cikin kogin Gungun Sarki ne a safiyar ranar Litinin.

 

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

A cewar Mayanan Gungun, ‘yan kungiyar sun fara kashe diyar dorinar ne da karfe 11 na safe, sannan suka kashe uwar dorinar da karfe 3 na rana. Daga nan ne suka kai gawar dorinar zuwa fadar Hakimin Gungu, Alhaji Kasimu Aliyu, inda aka fede namanta aka Kuma rarraba naman nata ga jama’ar Yankin har ma da wasu daga garin Yauri, Inji Mayanan Gungun Alhaji Nasir Sarki.

 

Hakazalika ya ce, “Al’ummar Masarautar Yauri dai sun ji dadi kan nasarar da aka samu kan kashe dorinar ita da diyarta saboda ta dauko hanyar hallaka jama’armu wannan al’amari ya yi ma duk dan yankin masarautar Yauri dadi. Haka kuma sun bayyana godiyarsu ga Gwamna Nasir Idris da Sarkin, Dakta Muhammad Zayyanu Abdullahi bisa wannan mataki da suka dauka na bada umurni na hallaka wannan dorinar ita da diyarta”.

 

Bugu da kari, Mayanan Gungun ya kara da cewa, “Wannan lamarin dai bai zo da mamaki ba, domin a mokonin baya an sha samun rahotannin hare-haren wannan dorinar har ta Kashe Mai-Gadin Lambun Sarkin Yauri, a cikin watan Satumbar 2024, wanda ke kamun kifi mai shekaru 60, mai suna Malam Usman Maigadi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 1
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci A Yi Bincike Tare Da Hukunta Wadanda Suka Kai Wa Motocin Kamfanin Kasar Hari A Pakistan

Next Post

Zirga-Zirgar Ababen Hawa Na Gudana Yadda Ya Kamata Yayin Hutun Mako Guda Na Sin

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

12 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

14 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

15 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

16 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

17 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

18 hours ago
Next Post
Zirga-Zirgar Ababen Hawa Na Gudana Yadda Ya Kamata Yayin Hutun Mako Guda Na Sin

Zirga-Zirgar Ababen Hawa Na Gudana Yadda Ya Kamata Yayin Hutun Mako Guda Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.