• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Masunta 31, 40 Sun Yi Ɓatan Dabo A Wani Harin ‘Yan Ta’adda A Borno

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla masunta 31 ne aka kashe yayin da wasu 40 suka yi batan dabo yayin da wasu ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP suka kai wani mummunan hari a Tunbun Rogo – wani kauye da ake kamun kifi a karamar hukumar Kukawa ta jihar Borno, a daren ranar Talata.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin a ranar Laraba ga LEADERSHIP a Maiduguri, Shugaban Kungiyar Dillalan Kifi ta Nijeriya, Mohammed Laminu, ya ce wannan mummunan labari ya tayar wa ‘ya’yan kungiyar da hankali.

  • Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Dawo Da Tsohon Taken Nijeriya
  • ‘Yansanda Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kwato Kudin Fansa A Kaduna

A cewar wani ganau da ya nemi a sakaya sunansa, ‘yan ta’addar sun kashe masunta 31, inda iyalai da dama ke jiran labarin ‘yan uwansu.

“Gawarwakin wadanda iftila’in ya rutsa da su, na jibge a cikin daji, yayin da sauran da suka gudu zuwa dazuzzuka suka fara dawowa da raunuka, suna karbar magani daga sansanin sojoji dake Cross Kauwa.

“’Yan ta’addan sun far wa yankin ne dauke da makamai, inda suka zagaye masuntan sannan suka bude wuta, harin ya faru ne bayan da sojoji suka umurci masuntan da su fice daga yankin, amma duk da bin umarnin da aka ba su, ‘yan ta’addan sai da suka far musu.”

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Majiyar ta ci gaba da cewa,”‘yan ta’addan ne suka tara mu, inda suka ce suna son yi mana wa’azi ne, sai kwamandansu ya bayar da umarnin a kashe mu, nan take suka kashe masunta 31, kuma sama da 40 daga cikinmu muka yi nasarar tserewa.

“Kwamandan ya umarci a hukunta daya daga cikin ‘yan ta’addan saboda ya bar wasu daga cikinmu sun gudu.”

Wadanda iftila’in ya afka mawa masunta ne daga garuruwan Monguno, Doron Baga, Cross Kauwa, da Baga.

Kawo yanzu dai babu wata sanarwa da hukumomin sojin Nijeriya ko wata hukumar tsaro suka fitar kan harin ba har ya zuwa lokacin rubuta wannan rahoto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Boko HaramBagaMayakan ISWAPSambisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Peng Liyuan Ta Yi Zanta Da Mai Dakin Shugaban Kasar Equatorial Guinea

Next Post

Rahoto Kan Yadda Aka Keta Hakkin Dan Adam A Kasar Amurka A Shekarar 2023

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

15 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

17 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

17 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

1 day ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Rahoto Kan Yadda Aka Keta Hakkin Dan Adam A Kasar Amurka A Shekarar 2023

Rahoto Kan Yadda Aka Keta Hakkin Dan Adam A Kasar Amurka A Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.