ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

by Abubakar Abba
9 months ago
Kaduna

Wani bincike da Jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa, ayyukan da ke gudanarwa a Tashar Jiragen Ruwa ta Kantudu da ke a jihar Kaduna sun ja baya matuƙa

A cewar binciken, hakan ya faru ne, saboda dakatar da gudanar da ayyukan zirga-zirgar Jiragen Ƙasa da ke tasowa daga Tashoshin Jiragen Ruwa na jihar Legas saboda ƙalubalen rashin tsaro da kuma yadda ambaliyar ruwan sama, ya lalata wani sashe na Titin Jirgin ƙasa.

  • Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin
  • Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

A shekarar 2018 Marigayi Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ne, ya ƙaddamar da Tashar.

ADVERTISEMENT

An tsara ta ne, domin sauke kayan da Jiragen Ruwa suka yo jiglarsu tare da kuma tura kayan a cikin sauƙi, zuwa ga guraren da aka tsara kaisu da kuma rage cunkoso a Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas, wanda hakan kuma zai taimaka masu motocin da za su yi safafar kayan .

Sai dai, bisa wasu bayanai da Jaridar LEADERSHIP ta samu sun bayyana cewa, Jiragen Ruwan sun gaza yin jigilar kaya daga Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas shekaru da dama da suka gabata zuwa Tashar ta kantudu da ke a jihar Kaduna, musamman saboda yawan aukuwar ayyukan ‘yan bindiga a jihar Neja da kuma yadda ambaliyar ruwan sama ta lalata wasu sansan hanyar layin Dogo da ke yankin Mokwa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Waɗannan matsalolin, sun sanya ake yin jigilar  kayan ta kan hanya, a manyan motoci, wanda hakan ya sanya masu ruwa da tsaki a fannin ke ci gaba da kokawa, saboda kuɗaɗen da suke kashewa masu yawa, wajen jigilar kayansu

wanda hakan ya saɓawa manufar ta kafa Tashodhin  Jiragen Ruwan ta kantudu.

Injiniya Kayode Opeifa Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ƙasa na ƙasa ya tabbatar da waɗannan matsalolin a taron 2025 Ƙungiyar ‘Yan Jarida Wakilai  da ke ɗauko rahotannin ɓangaren sufuri TCAN, da aka gudanar a jihar Legas.

A cewar Kayode, ƙalubalen rashin tsaro, a jihar Neja, hakan ya tilasta Hukumar dakatar da jigilar kayan ta hanyar amfani da Jirgin ƙasa zuwa Kaduna.

Sai dai ya bayyana cewa gwamnonin jihohin Neja da Kaduna, sun yi haɗaka domin lalubo da mafita kan lamarin.

Wani Babban Jami’i a Tashar ta kantudu da ke a jihar Kaduna wanda bai buƙaci a sakaya sunansa ya shedawa LEADERSHIP cewa, baya ga ƙalubalen rashin tsaro, ambaliyar ruwan sama da ta auku a jihar Nije, ta janyo yin gaba da wasu ƙarafan da Jirgin ƙasa ke bi, wanda hakan ya dates ɗaukacin duk wata zirga-zirgar Jiragen zuwa Tashar.

“Muna ci ga da jiran Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ƙasa ta ƙasa NRC, domin ta gyran hanyar ta layin Dogon, wanda kuma idan harkar tsaro ta ƙaru, hakan zai bai wa masu hada-hadar safarar kaya a Jiragen Ƙasan, su samu damar ci gaba da yi zuwa Tashar ta Kantudu, da ke a jihar ta Kaduna, “ A cewar babban jami’i.

Ya ƙara da cewa, yayin da ayyukan sufurin suka tsaya tska, hakan ya sanya ba a yin safarar kaya a cikin Jiragen zuwa Tashar.

Sai dai, wasu masu ruwa da tsaki a fannin sun bayyana fargabar da cewa, ci gaba da ɓata lokaci da ake yi na rashin yin amfani da Tashar hakan zai karya masu ƙwaiwa na ci gaba da yin amfani  da Tashar wajen yin safarar kayansu zuwa Tashar.

Bugu da ƙari, sun bayyana cewa, hakan zai kuma mayar da hannun Agogo bayan na ƙiƙarin Gwamnatin Tarayya na ci gaba da ɗaga darajar Tashoshin na Kandu, da aka samar a ƙasar, musamman wajen samar da sauƙin gudanar da hada-hadar kasuwanci a yankin Afirka.

Sai dai, duk da wannan ƙalubalen Hukumar ta NRC da kuma sauran gwamnonin jihohin da abin ya shafa, na kan yin aiki daomin sake dawo da zirga-ziragar kaya zuwa Tashar ta hanyar ƙara ƙarfafa tasaro da kuma sanya wasu ƙarafan na layin Dogo, da ambaliar ruwan saman, ta yi gaba da su.

Kaduna
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.