ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

by Sani Anwar
4 months ago
Tsafi

Shugaban kungiyar masu nakasa ta fuskar datsattsen lebe da handa na Nijeriya (NACLP), Farfesa Nnadozie Ugochukwu, ya bayyana rashin jin dadinsa, kan yadda ake amfani da yara masu nakasa a lebe wajen yin tsafi da su.

Ya bayyana kalubalen kiwon lafiya da ke da alaka da jariran da aka haifa a matsayin babban kalubale a Nijeriya, inda ya bayyana cewa; wasu lokutan ana ganin yaran da ke fama da wannan matsala a matsayin kamar ‘ya’yan da shedanu ke dauke da su, shi yasa mafi yawan lokuta ake sadaukar da su (Tsafi).

  • An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
  • An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

Da yake zantawa da manema labarai a taron kimiyya karo na 6 da aka gudanar da kuma taron shekara na 2025 (AGM), wanda ya gudana a babban asibitin kashi na kasa da ke Jihar Inugu, shugaban kungiyar ya shawarci mata masu juna biyu da su rika kula da zuwa awon ciki yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai a Nijeriya da ta fara ba da kulawa sosai wajen tunkarar kalubalen lafiyar Dan’adam da ke da alaka da jariran da aka haifa.

“Har yanzu, wannan babban kalubale ne a Nijeriya, domin kuwa ana ganin wadanda aka haifa da nakasa a lebe a matsayin jariran da shedanu ko aljanu ke dauke da su, wani lokacin kuma ana sadaukar da su ko a yi tsafi da su; wanda ko shakka babu, wannan batu ya haifar da rushewar gidaje da dama da kuma mutuwar aure.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

“A wajen jahilai, tsagaggen lebe lahani ne a kan makogwaro da lebe, amma idan akwai shinge tsakanin hanci da baki, ana kiran sa da suna handa. Wani abu ne da ba a san abin da yake kawo shi ba, amma kuma ana danganta shi da abubuwa da dama kamar karancin rashin sinadarin bitamin B.”

“Don haka, muna shawartar mata masu juna biyu da su mayar da hankali wajen yawan zuwa awon ciki, sannan kuma su rika shan magungunan da ake ba su na yau da kullum, ta yadda za a rage haihuwar masu dauke da wannan cuta.

“Hakika wannan babban abin takaici ne a cikin al’umma, shi yasa kwararrun likitoci, ma’aikatan jinya, jami’an jin dadin al’umma da likitocin makogwaro, hanci da kunne suka taru, domin ganin abin da za mu iya yi da zai kawo wa al’umma sauki tare da karfin tattalin arziki a tsakaninsu a wannan kasa”, in ji shi.

Har ila yau, da yake zantawa da manema labarai, Daraktan kula da lafiya na asibitin kashi na kasa da ke Jihar Inugu, Farfesa Emmanuel Iyidiobi ya bayyana cewa; kulawa da masu matsalar tsagaggen lebe, na daya daga cikin manyan manufofin da wannan asibiti ya sanya a gaba don ganin ya cimma, yana mai jaddada cewa; wani bangare ne na aikin tiyata, ya gara da cewa, wasu daga cikin sassan sun hada da kula da wadanda suka kone, tiyata da dai sauran makamantansu.

“Mun yi hadin gwiwa da kungiyar ‘Smile Train’ fiye da shekara goma da ta wuce, domin kula da marasa lafiya. Kazalika, zan iya fada muku cewa; bayanai sun nuna cewa, mun fi kowane asibiti a Nijeriya yawan yin wa marasa lafiya tiyata”.

“Don haka, ba wani abu ba ne na daban don mun karbi bakuncin wannan taro na bana, sannan kuma mun ji dadin yin hakan kwarai da gaske. Kazalika, me yasa muke yin hakan? Da farko dai, hakan ya yi daidai da muradun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

“Sannan, sabon kudirin nan na shugaban kasar game da kiwon lafiya, ya mayar da hankali tare da karfafa asibitoci wajen inganta harkokinsu ta hanyar horaswa da bincike ta yadda daga wasu kasashen na waje za a rika zuwa a matsayin yawon bude ido tare da neman lafiya a wannan kasa, shi yasa muka yanke shawarar tallafa wa taron ka’in da na’in”, in ji shi.

Har ila yau, a nata jawabin, mataimakiyar shugabar kungiyar ‘Smile Train’, Darakta a shiyyar Afirka, Madam Nkeiruka Obi ta ce; kungiyar ta yi imanin cewa; duk yaron da aka haifa da matsalar datsattsen lebe, ya cancanci samun cikakkiyar kulawa daga kwararru, wadanda suka samu horo a cikin gida Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Goron Sallah

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.