ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

by Sani Anwar
1 year ago
Tsafi

Shugaban kungiyar masu nakasa ta fuskar datsattsen lebe da handa na Nijeriya (NACLP), Farfesa Nnadozie Ugochukwu, ya bayyana rashin jin dadinsa, kan yadda ake amfani da yara masu nakasa a lebe wajen yin tsafi da su.

Ya bayyana kalubalen kiwon lafiya da ke da alaka da jariran da aka haifa a matsayin babban kalubale a Nijeriya, inda ya bayyana cewa; wasu lokutan ana ganin yaran da ke fama da wannan matsala a matsayin kamar ‘ya’yan da shedanu ke dauke da su, shi yasa mafi yawan lokuta ake sadaukar da su (Tsafi).

  • An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
  • An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

Da yake zantawa da manema labarai a taron kimiyya karo na 6 da aka gudanar da kuma taron shekara na 2025 (AGM), wanda ya gudana a babban asibitin kashi na kasa da ke Jihar Inugu, shugaban kungiyar ya shawarci mata masu juna biyu da su rika kula da zuwa awon ciki yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai a Nijeriya da ta fara ba da kulawa sosai wajen tunkarar kalubalen lafiyar Dan’adam da ke da alaka da jariran da aka haifa.

“Har yanzu, wannan babban kalubale ne a Nijeriya, domin kuwa ana ganin wadanda aka haifa da nakasa a lebe a matsayin jariran da shedanu ko aljanu ke dauke da su, wani lokacin kuma ana sadaukar da su ko a yi tsafi da su; wanda ko shakka babu, wannan batu ya haifar da rushewar gidaje da dama da kuma mutuwar aure.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

“A wajen jahilai, tsagaggen lebe lahani ne a kan makogwaro da lebe, amma idan akwai shinge tsakanin hanci da baki, ana kiran sa da suna handa. Wani abu ne da ba a san abin da yake kawo shi ba, amma kuma ana danganta shi da abubuwa da dama kamar karancin rashin sinadarin bitamin B.”

“Don haka, muna shawartar mata masu juna biyu da su mayar da hankali wajen yawan zuwa awon ciki, sannan kuma su rika shan magungunan da ake ba su na yau da kullum, ta yadda za a rage haihuwar masu dauke da wannan cuta.

“Hakika wannan babban abin takaici ne a cikin al’umma, shi yasa kwararrun likitoci, ma’aikatan jinya, jami’an jin dadin al’umma da likitocin makogwaro, hanci da kunne suka taru, domin ganin abin da za mu iya yi da zai kawo wa al’umma sauki tare da karfin tattalin arziki a tsakaninsu a wannan kasa”, in ji shi.

Har ila yau, da yake zantawa da manema labarai, Daraktan kula da lafiya na asibitin kashi na kasa da ke Jihar Inugu, Farfesa Emmanuel Iyidiobi ya bayyana cewa; kulawa da masu matsalar tsagaggen lebe, na daya daga cikin manyan manufofin da wannan asibiti ya sanya a gaba don ganin ya cimma, yana mai jaddada cewa; wani bangare ne na aikin tiyata, ya gara da cewa, wasu daga cikin sassan sun hada da kula da wadanda suka kone, tiyata da dai sauran makamantansu.

“Mun yi hadin gwiwa da kungiyar ‘Smile Train’ fiye da shekara goma da ta wuce, domin kula da marasa lafiya. Kazalika, zan iya fada muku cewa; bayanai sun nuna cewa, mun fi kowane asibiti a Nijeriya yawan yin wa marasa lafiya tiyata”.

“Don haka, ba wani abu ba ne na daban don mun karbi bakuncin wannan taro na bana, sannan kuma mun ji dadin yin hakan kwarai da gaske. Kazalika, me yasa muke yin hakan? Da farko dai, hakan ya yi daidai da muradun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

“Sannan, sabon kudirin nan na shugaban kasar game da kiwon lafiya, ya mayar da hankali tare da karfafa asibitoci wajen inganta harkokinsu ta hanyar horaswa da bincike ta yadda daga wasu kasashen na waje za a rika zuwa a matsayin yawon bude ido tare da neman lafiya a wannan kasa, shi yasa muka yanke shawarar tallafa wa taron ka’in da na’in”, in ji shi.

Har ila yau, a nata jawabin, mataimakiyar shugabar kungiyar ‘Smile Train’, Darakta a shiyyar Afirka, Madam Nkeiruka Obi ta ce; kungiyar ta yi imanin cewa; duk yaron da aka haifa da matsalar datsattsen lebe, ya cancanci samun cikakkiyar kulawa daga kwararru, wadanda suka samu horo a cikin gida Nijeriya.

Tsafi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Next Post
Goron Sallah

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.