ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Banki

Wata kotun hukunta manyan laifuka ta Jihar Legas da ke Ikeja ta gurfanar da wani tsohon manajan banki reshen Iju, Abiodun Sanni, a gidan yari bisa zargin damfarar Naira miliyan 122,011,441.

Hukumar Yaki Da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa, ta gurfanar da Sanni a gaban kuliya 16 da suka hada da karbar bashi ta hanyar karya, amfani da takardun karya da kuma sata.

  • Bankin Duniya Da IMF Na Kassara Tsarin Ilimin Jami’o’i A Nijeriya – ASUU
  • Karancin Kudin Shiga Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya

Lauyan masu shigar da kara na EFCC, O. Adewunmi, ya shaida wa kotun cewa Sanni ya aikata laifin ne a ranar 24 ga Fabrairu, 2020, a Legas.

ADVERTISEMENT

Adewunmi ya shaida wa kotun cewa wanda ake kara a lokacin yana manajan bankin Polaris Bank Limited reshen lju, ya samu rance ne a matsayin rancen kudi Naira miliyan 17, kan wani Bamgbose Tayo Taofia da ke kasuwanci da suna da salon Banut Haulage. .

Mai gabatar da kara ya bayyana cewa, an samu kudin ne daga bankin Polaris Bank Limited, ta hanyar karyar cewa bashin na da garantin ne a wani kayyade a asusun ajiya mai lamba 0071572791, kudin da ya kai Naira miliyan 111,540,380.52 mallakin Yinkus Multibiz Bentures da kuma mai ita, daya Misis Olayinka. Hannah Aderibigbe, ta amince a yi amfani da shi a matsayin jingina.

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

Haka kuma an zarge shi da rashin gaskiya da canza wani asusun ajiya na Polaris Bank Limited mai lamba 0071277522 akan kudi Naira miliyan 15, 011,441.00 (Miliyan Goma Sha Biyar, Dubu Sha daya, Dari Hudu da Arba’in da Daya) mallakar Atolagbe Joshua Tinuoye, zuwa amfani da shi.

Sai dai wanda ake tuhumar ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.

Lauyan mai gabatar da kara, ya bukaci kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake kara a gidan gyaran hali, har zuwa lokacin da za a fara shari’a.

“Ya Ubangiji, mai gabatar da kara ya yi niyyar gabatar da shaidu 10 game da wannan shari’a kuma muna rokon kotu ta tsare wanda ake kara a gidan yari”, in ji Adewunmi.

Sai dai lauyan da ake kara, Osho Oludoshu, ya shaida wa kotun cewa ya shigar da bukatar neman beli a madadin wanda yake karewa.

A wani takaitaccen hukunci mai shari’a Olubunmi Abike-Fadipe, ta dage ci gaba da sauraron karar tare da bayar da umarnin mika bukatar belin ga kotu kafin ranar da za a fara shari’ar.

“Na dage shari’ar zuwa Match 6 da 19, 2025, kuma na tsare wanda ake kara a gidan gyaran hali. Suna da damar gabatar da takardar neman beli kafin ranar shari’arsa,” in ji alkalin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC
Labarai

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Manyan Labarai

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

November 11, 2025
Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako

Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako

November 11, 2025
APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.