ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

by Abubakar Abba
2 years ago
Wake

Wake na daya daga cikin amfanin gonar da aka dakatar da shigar da da shi daga Nijeriya zuwa Tarayyar Turai.

Wasu kwararru sun yi gargadin cewa, akwai yiwuwar farashin Wake ba zai sauka ba a wannan kasa da muke ciki.

  • Kakar Da Ta Fi Dacewa Da Noman Wake A Nijeriya
  • Nazari Kan Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Shuka Wake A Nijeriya

Kazalika, Cibiyar Kula da Fitar da Kayayyaki Kasashen Waje ta Kasa (NEPC) ta sanar da cewa, Nijeriya na noma Wake mai dimbin yawa; wanda ya kai kimanin kashi 58 cikin 100 na yawan wanda ake bukata a duniya.

ADVERTISEMENT

Sai dai, wasu matsaloli da suka hada da ayyukan ‘yan bindigar daji, yawan rikice-rikice a tsakanin manoma da makiyaya da sauran makamantansu, an danganta su a matsayin manyan kalubalen da ke jawo rashin noman Waken da dama a Nijeriya.

Bugu da kari, akwai kuma kalubalen rashin kayan aiki; da suka hada da samar da wurin adana shi da rashin yin amfani da dabarun zamani, wanda hakan ya jawo rashin samar da wadatuwar sa a fadin wannan kasa.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Shugaban Kungiyar Manoma na Kasar, reshen Jihar Kano (AFAN); Alhaji Abdulrasheed Magaji Rimin Gado ya sanar da cewa, sauyin yanayi da kuma matsalar rashin tsaro, sun yi matukar taka muhimmiyar rawa wajen kawo raguwar noman wannan Wake.

An ruwaito cewa, Jamhuriyar Nijar; na tura kimanin kashi 45 cikin 100 na Waken da take nomawa zuwa wasu jihohin Arewacin Nijeriya, inda ake hada-hadar kasuwacninsa ta hanyar musayar Naira da kuma takardar kudin CFA, wanda hakan ko kadan baya taimakawa wannan fanni.

Magaji ya ci gaba da cewa, manyan dillalansa ba sa iya shigo da shi cikin wannan kasa, sakamakon matsalar samun kudaden musaya da ba sa iya samu.

Ya kara da cewa, lamuran na ci gaba da kara munana; musamman idan aka yi la’akari da wani rahoto da ya riske mu da ke nuna cewa, Jamhuriyar ta Nijar ta dakatar da fitar da amfanin gona daga kasar zuwa wasu kasashe, ciki har da Nijeriya.

A cewarsa, hakan ba zai bari farashinsa da sauran kayan amfanin gona su ragu ba.

Ya sanar da cewa, akwai matukatar bukatar a bai wa noman rani muhimmanci, musamman don cike gibin da aka samu a noman damina na bana.

Kazalika, ya sanar da cewa, ya zama wajibi gwamnati ta kayyade farashi, musamman a kan Wake domin samar da wadatuwarsa; cikin kuma farashi mai sauki.

Shi ma, wani babban dila a Kasuwar Hatsi ta kasa da kasa a Kasuwar Dawanau ta Jihar Kano, Alhaji Musa Gawuna ya bayyana cewa; ba a noman Wake da yawa, duk kuwa da matukar bukatar da ake da shi.

A cewarsa, wasu manoman; musamman na Waken, na kauracewa gonakinsu, saboda yawan samun rikice-rikicen manoma da makiyaya, wanda hakan ya dakatar da manoman daga yin nomansa kamar yadda aka yi tsammani.

Rahotannin sun ce, mahukuntan soji na kasar Nijar, sun dakatar da fitar da Shinkafa da sauran amfanin gona zuwa sauran kasashen duniya.

Sun dauki wannan matakin ne, biyo bayan barazanar da kungiyar ECOWAS ta yi wa mahukuntan kasar na cewa, tilas ne su mayar da kasar kan turbar mulkin dimokradiyya; bayan juyin mulkin da suka yi a kasar a shekarar da ta gabata.

Wake
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.