• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kusa Raba Gari Tsakanin Mbappe Da PSG

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Mbappe

LABARAI MASU NASABA

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Za a iya cewa idan za a yi la’akari da abubuwan da suka faru a wasan karshe da Paris St-Germain ta buga, akwai alamun cewa za a samu abubuwan ban mamaki a ‘yan watannin da suka rage wa Kylian Mbappe a kungiyar.

Mbappe ya amince ya koma Real Madrid a wannan bazarar, kuma duk da cewa PSG ba ta tabbatar da hakan a hukumance ba alamu sun fara nuna cewa ta fara shirin rayuwa ba tare da dan wasan ba.

  • Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri
  • Ana Amfani Da Na’urar Hakar Mai Ta Zamani Da Kamfanin Sin Ya Kera A Uganda

A karawar da ta yi da Monaco a ranar Juma’ar da ta gabata, inda wasan ya kare babu ci, an cire Mbappe ne a lokacin hutun rabin lokaci amma maimakon zama tare da takwarorinsa a bencin PSG, Mbappe ya zabi ya zauna tare da mahaifiyarsa a cikin ‘yan kallo.

Yanzu dai an sauya Mbappe a wasanni biyu a jere, inda aka maye gurbinsa bayan mintuna 65 a wasan da suka tashi 1-1 da Rennes bayan ya kasa zura kwallo a raga a wasan.

Sai dai kociyan kungiyar ta Paris Saint German, Luis Enrikue, ya bayyana cewa ko ba-jima ko ba-dade sai sun fara sabawa da wasa ba tare da dan wasa Kylian Mbappe ba a kungiyar.

Dan wasa Mbappe ya ci wa PSG kwallaye 26 a dukkan gasa a kakar wasa ta bana, inda 21 daga cikinsu suka zo a gasar Ligue 1 wanda ya sa ya zama kan gaba a jerin masu cin kwallo a gasar.

PSG dai tana kan hanyar kare kambunta na gasar kasar Faransa inda take da tazarar maki tara tsakaninta da Brest wadda ke a matsayi na biyu amma kuma yayin da nasarorin cikin gida suka zo cikin sauki ga PSG a karkashin mallakar ‘yan Katar, samun nasara a gasar zakarun Turai ya faskara.

Idan aka yi la’akari da tarihin bajintarsa a gasar, da alama PSG za ta yi wa kanta sakiyar da babu ruwa idan har ba ta samu abin da ya kamata ba daga shararren dan wasan na duniya kafin ya tafi.

Sai dai shima Mbappe ya ce ba shi da matsala da kociyan kungiyar ta PSG Luis Enrikue, ya bayyana haka ne a ranar da ya zura kwallaye biyu a gasar cin kofin zakarun Turai da suka doke Real Sociedad wanda hakan ya sanya PSG ta ketara zuwa zagayen dab da na kusa da na karshe.

Tun bayan da ya bayyana aniyarsa ta barin Parc des Princes, masu bibiyar harkar kwallon kafa sun sanya alamar tambaya kan zamantakewarsa da Enrikue, inda ake ajiye dan wasan a benci ko kuma an cire shi da wuri, musamman wasannin PSG uku na baya-bayan nan a gasar Ligue 1.

Amma Mbappe ya ce ” A koyaushe ina son buga gasar Zakarun Turai, gasa ce mai matukar muhimmanci. Ba zan taba zama dan wasan dake buya ba sannan dangantaka ta da kocina na da kyau, babu matsala ko da mutane za su yi tunanin cewa akwai. Ina da matsaloli da yawa amma kocin ba ya cikinsu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray
Wasanni

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid
Wasanni

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Bayyana Matsayarta Kan Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Bayyana Matsayarta Kan Batun Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.