• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kusa Raba Gari Tsakanin Mbappe Da PSG

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
An Kusa Raba Gari Tsakanin Mbappe Da PSG
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

Za a iya cewa idan za a yi la’akari da abubuwan da suka faru a wasan karshe da Paris St-Germain ta buga, akwai alamun cewa za a samu abubuwan ban mamaki a ‘yan watannin da suka rage wa Kylian Mbappe a kungiyar.

Mbappe ya amince ya koma Real Madrid a wannan bazarar, kuma duk da cewa PSG ba ta tabbatar da hakan a hukumance ba alamu sun fara nuna cewa ta fara shirin rayuwa ba tare da dan wasan ba.

  • Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri
  • Ana Amfani Da Na’urar Hakar Mai Ta Zamani Da Kamfanin Sin Ya Kera A Uganda

A karawar da ta yi da Monaco a ranar Juma’ar da ta gabata, inda wasan ya kare babu ci, an cire Mbappe ne a lokacin hutun rabin lokaci amma maimakon zama tare da takwarorinsa a bencin PSG, Mbappe ya zabi ya zauna tare da mahaifiyarsa a cikin ‘yan kallo.

Yanzu dai an sauya Mbappe a wasanni biyu a jere, inda aka maye gurbinsa bayan mintuna 65 a wasan da suka tashi 1-1 da Rennes bayan ya kasa zura kwallo a raga a wasan.

Sai dai kociyan kungiyar ta Paris Saint German, Luis Enrikue, ya bayyana cewa ko ba-jima ko ba-dade sai sun fara sabawa da wasa ba tare da dan wasa Kylian Mbappe ba a kungiyar.

Dan wasa Mbappe ya ci wa PSG kwallaye 26 a dukkan gasa a kakar wasa ta bana, inda 21 daga cikinsu suka zo a gasar Ligue 1 wanda ya sa ya zama kan gaba a jerin masu cin kwallo a gasar.

PSG dai tana kan hanyar kare kambunta na gasar kasar Faransa inda take da tazarar maki tara tsakaninta da Brest wadda ke a matsayi na biyu amma kuma yayin da nasarorin cikin gida suka zo cikin sauki ga PSG a karkashin mallakar ‘yan Katar, samun nasara a gasar zakarun Turai ya faskara.

Idan aka yi la’akari da tarihin bajintarsa a gasar, da alama PSG za ta yi wa kanta sakiyar da babu ruwa idan har ba ta samu abin da ya kamata ba daga shararren dan wasan na duniya kafin ya tafi.

Sai dai shima Mbappe ya ce ba shi da matsala da kociyan kungiyar ta PSG Luis Enrikue, ya bayyana haka ne a ranar da ya zura kwallaye biyu a gasar cin kofin zakarun Turai da suka doke Real Sociedad wanda hakan ya sanya PSG ta ketara zuwa zagayen dab da na kusa da na karshe.

Tun bayan da ya bayyana aniyarsa ta barin Parc des Princes, masu bibiyar harkar kwallon kafa sun sanya alamar tambaya kan zamantakewarsa da Enrikue, inda ake ajiye dan wasan a benci ko kuma an cire shi da wuri, musamman wasannin PSG uku na baya-bayan nan a gasar Ligue 1.

Amma Mbappe ya ce ” A koyaushe ina son buga gasar Zakarun Turai, gasa ce mai matukar muhimmanci. Ba zan taba zama dan wasan dake buya ba sannan dangantaka ta da kocina na da kyau, babu matsala ko da mutane za su yi tunanin cewa akwai. Ina da matsaloli da yawa amma kocin ba ya cikinsu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Jamhuriyar Congo: Ra’ayin Sabon Mulkin Mallaka Ba Shi Da Tushe

Next Post

Kasar Sin Ta Bayyana Matsayarta Kan Batun Kare Hakkin Dan Adam

Related

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City
Wasanni

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

19 hours ago
Boniface
Wasanni

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

3 days ago
Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong
Wasanni

Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong

4 days ago
Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0
Wasanni

Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0

6 days ago
Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Wasanni

Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

6 days ago
Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?
Wasanni

Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?

6 days ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bayyana Matsayarta Kan Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Bayyana Matsayarta Kan Batun Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.