• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kusa Raba Gari Tsakanin Mbappe Da PSG

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
An Kusa Raba Gari Tsakanin Mbappe Da PSG
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

Za a iya cewa idan za a yi la’akari da abubuwan da suka faru a wasan karshe da Paris St-Germain ta buga, akwai alamun cewa za a samu abubuwan ban mamaki a ‘yan watannin da suka rage wa Kylian Mbappe a kungiyar.

Mbappe ya amince ya koma Real Madrid a wannan bazarar, kuma duk da cewa PSG ba ta tabbatar da hakan a hukumance ba alamu sun fara nuna cewa ta fara shirin rayuwa ba tare da dan wasan ba.

  • Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri
  • Ana Amfani Da Na’urar Hakar Mai Ta Zamani Da Kamfanin Sin Ya Kera A Uganda

A karawar da ta yi da Monaco a ranar Juma’ar da ta gabata, inda wasan ya kare babu ci, an cire Mbappe ne a lokacin hutun rabin lokaci amma maimakon zama tare da takwarorinsa a bencin PSG, Mbappe ya zabi ya zauna tare da mahaifiyarsa a cikin ‘yan kallo.

Yanzu dai an sauya Mbappe a wasanni biyu a jere, inda aka maye gurbinsa bayan mintuna 65 a wasan da suka tashi 1-1 da Rennes bayan ya kasa zura kwallo a raga a wasan.

Sai dai kociyan kungiyar ta Paris Saint German, Luis Enrikue, ya bayyana cewa ko ba-jima ko ba-dade sai sun fara sabawa da wasa ba tare da dan wasa Kylian Mbappe ba a kungiyar.

Dan wasa Mbappe ya ci wa PSG kwallaye 26 a dukkan gasa a kakar wasa ta bana, inda 21 daga cikinsu suka zo a gasar Ligue 1 wanda ya sa ya zama kan gaba a jerin masu cin kwallo a gasar.

PSG dai tana kan hanyar kare kambunta na gasar kasar Faransa inda take da tazarar maki tara tsakaninta da Brest wadda ke a matsayi na biyu amma kuma yayin da nasarorin cikin gida suka zo cikin sauki ga PSG a karkashin mallakar ‘yan Katar, samun nasara a gasar zakarun Turai ya faskara.

Idan aka yi la’akari da tarihin bajintarsa a gasar, da alama PSG za ta yi wa kanta sakiyar da babu ruwa idan har ba ta samu abin da ya kamata ba daga shararren dan wasan na duniya kafin ya tafi.

Sai dai shima Mbappe ya ce ba shi da matsala da kociyan kungiyar ta PSG Luis Enrikue, ya bayyana haka ne a ranar da ya zura kwallaye biyu a gasar cin kofin zakarun Turai da suka doke Real Sociedad wanda hakan ya sanya PSG ta ketara zuwa zagayen dab da na kusa da na karshe.

Tun bayan da ya bayyana aniyarsa ta barin Parc des Princes, masu bibiyar harkar kwallon kafa sun sanya alamar tambaya kan zamantakewarsa da Enrikue, inda ake ajiye dan wasan a benci ko kuma an cire shi da wuri, musamman wasannin PSG uku na baya-bayan nan a gasar Ligue 1.

Amma Mbappe ya ce ” A koyaushe ina son buga gasar Zakarun Turai, gasa ce mai matukar muhimmanci. Ba zan taba zama dan wasan dake buya ba sannan dangantaka ta da kocina na da kyau, babu matsala ko da mutane za su yi tunanin cewa akwai. Ina da matsaloli da yawa amma kocin ba ya cikinsu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Jamhuriyar Congo: Ra’ayin Sabon Mulkin Mallaka Ba Shi Da Tushe

Next Post

Kasar Sin Ta Bayyana Matsayarta Kan Batun Kare Hakkin Dan Adam

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

19 hours ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

4 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

5 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

5 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

6 days ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bayyana Matsayarta Kan Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Bayyana Matsayarta Kan Batun Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Mbappe

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.